Coronavirus: Har yanzu gwamnati na neman wadanda suka hau jirgi tare da dan Italiya ya kawo cutar Najeriya

Coronavirus: Har yanzu gwamnati na neman wadanda suka hau jirgi tare da dan Italiya ya kawo cutar Najeriya

Har ila yau, gwamnatin tarayya tana cigaba da kokarin gano fasinjoji 155 da suka hau jirgi zuwa Nigeria tare da dan kasar Italiyan da aka tabbatar yana dauke da cutar coronavirus da ya shigo kasar.

Ministan kiwon lafiya, Osagie Ehanire ya bayyana hakane ga manema labarai a Abuja inda yace fasinjoji 156 suka hau jirgi tare da dan kasar Italiyan.

Daily Trust ta ruwaito cewa sabanin abinda ake samu daga wasu kasashe, ba’a bayyana sunan dan Italiyan mai dauke da cutar ga Jama’a ba.

Ministan yace ba’a gano wasu daga cikin fasinjojin da suka hau jirgi tare da dan Italiyan ba saboda ba’a samu bayanai daga garesu ba yadda ya kamata

Yace: “Ba za mu iya kayyade adadin wadanda ya hadu da su ba, Amma wadanda muke da tabbaci akansu sune fasinjoji 156 da suke tare dashi a jirgin, kuma ana bibiyansu, ana magana dasu kuma suna bada hadin kai."

“Muna fuskantar kananan kalubale. Wasu daga cikinsu sun bada lambobin waya mara aiki ko kuma idan an kira aji a kashe. Akwai kuma wadanda basu da wayar, ko kuma sabbi ne a kasar."

“Ba’a musu rajista da wani kamfanin wayar tarho ba, amma akwai hanyoyin da za’a nemosu. Wadand kuma a suka shigo dan ziyarar kwana daya ko biyu tuni sun bar kasar,”a cewar sa.

Ehanire yace tun lokacin da aka tabbatar da bullowar cutar ta farko, gwamnatin tarayya ta sa kai dan ganin ta takaita yaduwar cutar.yace har izuwa jiya ba’a samu Karin sabbin wadanda suka kamu da cutar ba a Nigeria.

Coronavirus: Har yanzu gwamnati na neman wadanda suka hau jirgi tare da dan Italiya ya kawo cutar Najeriya
Coronavirus
Asali: Twitter

A bangare guda, Akalla mutane 3000 sun mutu kawo yanzu a sakamakon cutar coronavirus da ta barke a kasar Sin. Wannan cuta ta fito ne a Yankin Wuhan, kafin cutar ta fara zagaya Duniya.

Kawo yanzu kimanin mutane 80,000 suka kamu da wannan cuta a fadin kasar Sin da kuma kimanin 4000 a ksar Koruya ta kudu.

Bullowar cutar a kasar Koriya ta kudu, inda itace mafi girma bayan Kasar Sin da cutar ta fito.

Ga jerin kasashe 66 da cutar ta bulla yanzu:

1. Afghanistan

2. Algeria

3. Australiya

4. Austria

5. Azerbaijan

6. Bahrain

7. Belgium

8. Brazil

9. Cambodiya

10. Sin

11. Czech

12. Canada

13. Croatia

14. Denmark

15. Dominica

16. Ecuador

17. Misra

18. Faransa

19. Geogiya

20. Jamus

21. Greece

22. Hong Kong

23. Iceland

24. Indiya

25. Indonisiya

26. Iraqi

27. Iran

28. Izraila

29. Italiya

30. Japan

31. Kuwait

32. Lebannon

33. Lithunia

34. Luxewmborg

35. Macau

36. Malayssiya

37. Mexico

38. Nepal

39.Holand

40. New Zealand

41. Najeriya

42. North Macedoniya

43. Norwway

44. Oman

45. Pakistan

46. Fillibin

47. Tunisiya

48. Jordan

49. Qatar

50. Romaniya

51. Rasha

52. San Marino

53. Singapore

54. Saudiyya

55. Koriya ta kudu

56. Sifen

57. Sri Lanka

58. Senegal

59. Sweden

60. Switzerland

61. Taiwan

62. Thailand

63. UAE

64. Birtanniya

65. Amurka

66. Vietnam

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel