Coronavirus: An killace yan kasar Sin 3 a jihar Plateau
An killace yan kasar Sin uku da ake zargin suna dauke da cutar coronavirus a karamar hukumar wase dake jihar Plateau, tsakiyar Najeriya.
Kwmaishanan kiwon lafiyar jihar, Nimkong Ndam, wanda tabbatar da hakan ya ce yan kasar Sin sin sun shiga jihar ne ranar Jumaa daga kasar Habasha. Sun zo jihar aikin hkar maadinai.
Ya ce tuni an killaceus a wata cibiya domin likitoci da masan kiwon lafiya su gudanar da bincike kansu.
Mun kawo muku rahoton cewa Ministan lafiya, Dr Osagie Ehanire, ya tabbatar da bullar cutar Coronavirus mai kisa a wata sanarwa da ya fitar a yau Juma'ar nan 28 ga watan Fabrairu.
A yadda sanarwar ta nuna, cutar ta shafi wani dan kasar Italiya ne wanda yake aiki a Najeriya, wanda ya dawo daga birnin Milan ya shigo Legas a ranar 25 ga watan Fabrairu.
An tabbatar da cutar a jikinshi, bayan gabatar da gwaje-gwaje a babban asibitin koyarwa na jami'ar Legas, a fannin binciken cututtuka.

Asali: Twitter
Ma'aikatar lafiyan ta tabbatar da cewa, mutumin yana nan yana karbar magani, kuma yana samun sauki a hankali a hankali.
Sanarwar ta kara da cewa, gwamnatin Najeriya karkashin ma'aikatar lafiya na iya bakin kokarinta wajen daukar mataki akan yaduwar cutar.
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Gwamnatin jihar Legas ta ce jamianta sun bazama neman dukkan wadanda dan kasar Italiyan da ya kawo cutar Najeriya ya hadu da su tun ranar da ya shigo.
Kwamishanan kiwon lafiyar jihar, Farfesa Akin Abayomi, ya bayyana hakan inda ya ce an kebance mutumin kuma ana kula da shi.
Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng