Hana bara a Kano: Sheikh Isa Pantami ya bayyana matsayinsa

Hana bara a Kano: Sheikh Isa Pantami ya bayyana matsayinsa

- Ministan harkokin sadarwa, Dakta Isa Ali Ibrahim Pantami, ya bayyana rashin amincewarsa da malaman addinin Islama da ke sukar dokar hana bara a jihar Kano

- Pantami, shehin malamin addinin Islma kafin a bashi minista, ya yi kira ga malaman addinin a kan su rungumi tsarin tattauna wa domin warware kowacce matsala

- Ministan ya bayyana hakan ne yayin da yake amsa tambayoyin manema labarai a wurin wani taron shirin yaye dalibai da kwalejin kimiyya ta Kano ta shirya

A ranar Juma'a ne ministan harkokin sadarwa, Dakta Isa Ali Ibrahim Pantami, ya bayyana rashin amincewarsa da malaman addinin Islama da ke sukar dokar hana bara a jihar Kano da gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya kaddamar.

Ministan ya bayyana matsayarsa ne yayin da yake amsa tambayoyin manema labarai jim kadan bayan ya kammala gabatar da takarda a wurin wani taron shirin yaye dalibai da kwalejin kimiyya ta Kano (Kano State Polytechnic) ta shirya ranar Juma'a.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Abba Anwar, sakataren yada labaran gwamnan jihar Kano, ya fitar.

Hana bara a Kano: Sheikh Isa Pantami ya bayyana matsayinsa
Sheikh Isa Pantami; ministan sadarwa
Asali: UGC

"A fahimtar da nake da ita a kan wannan batu, ba daidai bane a wurin malaman addini su fito suna kalubalantar gwamna haka kawai. Kamata ya yi su zo a zauna tare da su domin nemo mafita a kan lamarin.

DUBA WANNAN: Hukuncin kotu: An kashe mayakan kungiyar Boko Haram 10 ta hanyar bude musu wuta

"Saboda babu shakka mayar da yaran da ke bara makaranta shine mafi alheri a garesu, ga iyayensu da ma al'umma baki daya. A bangaren gwamnati, alhakin shugaba ne ya tabbatar da cewa jama'arsa sun samu rayuwa mai nagarta," a cewar Pantami, kamar yadda ya ke a cikin sanarwar da Anwar ya fitar.

Pantami, fitaccen malamin addinin Islma kafin ya zama minista, ya yi kira ga malaman addinin a kan su rungumi tsarin tattauna wa domin warware kowacce matsala. "Amma fa shawara ce kawai," in ji Pantami.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng

Tags: