Iran ta fadi hukuncin da za a yi wa masu yada labaran karya kan Coronavirus

Iran ta fadi hukuncin da za a yi wa masu yada labaran karya kan Coronavirus

Gwamnatin kasar Iran ta yi barazanar yi wa duk wanda aka kama yana yada labaran karya a kan cutar Coronavirus bulala tare da aike wa da shi gidan yari. Cutar a halin yanzu ya kashe mutane 26 a Iran.

Mai magana da yawun kwamitin shari'a na majalisar kasar, Hassan Norouzi ya ce duk wanda aka samu yana yada karya zai fuskanci hukuncin shekaru uku a gidan yari tare da bulala kamar yadda shari'a ta tanada.

Jaridar Tehran Times ta ruwaito cewa Norouzi ya ce, "Yada labaran karya a kan Coronavirus zai janye fargaba tsakanin mutane. Hakan kuma zai iya janyo abubuwa su tabarbare a kasar."

Iran ta fadi hukuncin da za a yi wa masu yada labaran karya kan Coronavirus
Iran ta fadi hukuncin da za a yi wa masu yada labaran karya kan Coronavirus
Asali: Twitter

Nourouzi ya kara da cewa a halin yanzu an kama mutane 24 suna yada jita-jita a kan kwayar cutar kuma za su fuskanci hukuncin da Shari'a ta tanada.

DUBA WANNAN: Yanzu-yanzu: Wani mutum ya sake daka tsalle ya fada ruwa a Legas (Hotuna)

A wani rahoton, Iran ta tabatar da mutuwar mutane bakwai sakamakon kamuwa da cutar ta Coronavirus cikin sa'o'i 24 a jiya wadda hakan na nuna cewa adadin wadanda suka mutu ya kai 26 wadda shine mafi yawa bayan wadanda suka mutu a China.

An kuma tabbatar cewa wasu karin mutane 106 sun kamu da cutar wadda hakan na nuna cewa jimlar wanda suka kamu da cutar ya kai 245 a kamar yadda mai magana da yawun hukumar Kianoush Jahanpour ya fadi yayin taron majalisar gwamnatin kasar.

Kazalika, a karo na farko an samu bullar kwayar cutar na Coronavirus a Legas Nigeria.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164