Zaratan Sojojin Najeriya sun hallaka Alkalin Alkalan kungiyar Boko Haram

Zaratan Sojojin Najeriya sun hallaka Alkalin Alkalan kungiyar Boko Haram

Dakarun rundunar Sojojin Najeriya sun kashe babban Alkalin kungiyar ta’addanci na Boko Haram, Akalin Alkalai Muhammad Shuwa a yayin wani samame da suka kaddamar a yankin tafkin Chadi.

Jaridar Sahara Reporters ta ruwaito wani bincike ya tabbatar da mutuwar akalla kwamandojin kungiyar guda 25 a cikin watanni biyu da suka gabata a sakamakon kara kaimi da wajen yaki da ta’addanci da rundunar Soji arewacin tafkin Chadi ta yi.

KU KARANTA: Tsuguni bata kare ba: EFCC ta tasa keyar ‘Mamar Boko Haram’ a kan zambar N42m

Wasu majiyoyi sun bayyana ma jaridar PRNigeria cewa yan ta’adda da daman a ta arcewa zuwa cikin kasashen Chadi, Nijar da Kamaru sakamakon mace mace da ake yawan samu a sansanonin Boko Haram a dalilin bamabamai da suke binnewa a zagaye da sansanonin, musamman bayan harin jiragen Soji.

“Wasu yan kasashen waje guda biyu dake daukan nauyin yan ta’adda sun mutu a yayin harin hadin gwiwa tsakanin jiragen yakin Najeriya da dakarun Sojin kasa a wani sansanin Boko Hara. Yawancin bakin hauren kwamandojin sun tsere, suka bar yan kasa.” Inji shi.

A wani labarin kuma, Hukumar rundunar Sojan sama ta bayyana cewa jiragenta dake yaki da ta’addanci a yankin jahar Borno masu sunan Rattle Snake 3 sun yi aman wuta a kan wasu gine gine da mayakan Boko Haram ke amfani dasu wajen fakewa.

Mai magana da yawun rundunar, Ibikunle Daramola ne ya bayyana haka a ranar Talata, inda yace jiragen Rattle Snake suna lalata sansanonin tare da kayayyakin aikin Boko Haram a yankunan Garin Malona da Parisu, duk a cikin dajin Sambisa.

Daramola ya ce a ranar 23 da 24 na watan Feburairu ne Sojojin rundunar Sojan sama dake sarrafa jiragen yakin suka tashi sansanonin biyu a cikin yakin da gwamnatin Najeriya ke yi da yan ta’adda karkashin Operation Lafiya Dole a yankin Arewa maso gabashin Najeriya.

“Mun kai harin ne bayan samun sahihan bayanai dake tabbatar da mayakan Boko Haram da suka kaddamar da hare hare a garin Garkidan jahar Adamawa sun fito ne daga sansanonin a cikin Sambisa

“Wannan ne yasa rundunar Sojan sama ta tura jiragen yakinta don su yi aman wuta a sansanonin tare da lalata dukkanin gine ginen dake cikinsu da kuma kayan aikinsu da makamansu dake jibge a wajen, kuma daga karshe mun hangesu sun kama da wuta duka.” Inji shi.

Ku biyo mu a https://facebook.com/legitnghausa

ko a http://twitter.com/legitnghausa

KU LATSA: Hanyar sauko da sabuwar manhajar jaridar Legit.com Hausa cikin sauki

Ga masu shawara ko korafi, a same mu a labaranhausa@corp.legit.com

Sanarwa na musamman: Shafin NAIJ Hausa ya koma Legit Hausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel