Wata mata ta haifi 'yan tagwaye a layin karbar tallafi a Jigawa

Wata mata ta haifi 'yan tagwaye a layin karbar tallafi a Jigawa

- Wata mata ta haifa tagwaye a yayin da take kan bin layin karbar tallafin N-Power a jihar Jigawa

- Wata majiya ta sanar da cewa matar ta haifi yaro daya ne a lokacin da ake tantanceta inda ta kara sunkoto daya bayan an kaita wani gidan biredi da ke makwabtaka da wajen

- A jawabin shugaban shirin bada tallafin na N-Power, Malam Bala Chamo ya ce mutane 14,000 ne suka amfana da tallafin naira dubu biyar-biyar din

Wata baiwar Allah ta haifa tagwaye a lokacin da take kan bin layin karbar tallafin N-Power a kofar fadar hakimin Aujara, Malam Aminu Danmalam.

Matar mai suna Khadija Abubakar na da shekaru 35 kuma tana sana’ar kuli-kuli ne. Ta je karbar tallafin ne daga kauyen Gorarun inda ta haifi tagwayen yara maza a wajen.

Hakimin garin Aujara, Malam Aminu Danmalam, ya tabbatar da aukuwar lamarin ga manema labarai.

Wata mata ta haifi 'yan tagwaye a layin karbar tallafi a Jigawa
Wata mata ta haifi 'yan tagwaye a layin karbar tallafi a Jigawa
Asali: UGC

Wata majiya ta sanar da cewa matar ta haifi yaro daya ne a lokacin da ake tantanceta. Ganin hakan ne yasa aka hanzarta kai ta wani gidan burodi da ke da makwabtaka da wajen inda ta sake haifo wani dan.

DUBA WANNAN: A garin neman gira: Matashi ya dirki kwayoyin karin kuzari, ya mutu yana lalata da budurwa

A jawabin shugaban shirin bada tallafin na N-Power, Malam Bala Chamo ya ce mutane 14,000 ne suka amfana da tallafin naira dubu biyar-biyar yayin da kuma mutane dubu dari ne za zu amfana da tallafin a jihar Jigawa.

Ya ce, kafin wannan lokacin, a baya ana ba mata 65,229 tallafin amma sai aka kara mata 34,771.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng