NAF ta kashe manyan shugabannin ISWAP a Borno

NAF ta kashe manyan shugabannin ISWAP a Borno

Rundunar Sojojin Saman Najeriya (NAF) a jiya ta ce ta kashe wasu muhimman shugabannin kungiyar slamic State of West Africa Province (ISWAP) a Jubillaram da Alinwa a arewacin Borno.

Wannan na zuwa ne bayan da dakarun sojojin Operation Hadarin Daji a Zamfara suka kashe 'yan bindiga 13 kuma suka kama wasu takwas a jihar Zamfara.

Direktan watsa labarai na NAF, Ibikunle Daramola a jiya a Abuja ya ce dakarun mayakan sama (ATF) na Operation Lafiya Dole karkashin atisayen Operation Rattle Snake III sun kai wa shugabanin ISWAP hari a lokacin da suka hadu wurin taro bayan samun bayannan sirri.

DUBA WANNAN: Atiku ya yi magana a kan harin da Boko Haram ta kai Adamawa

Sai dai sanarwar ba ta fadi adadin wadanda aka kashe ba da mukamansu a kungiyar amma ta kara da cewa: "An kai harin ne bayan samun bayyanan sirri da ke nuna wasu muhimman shugabanin ISWAP sun hadu domin yin taro a wurare biyu a Jubillaram da Alinwa a karamar hukumar Marte.

"Kazalika, dakarun na ATF sun kai hare-hare a wurare daban-daban inda suka yi raga-raga da wuraren taron 'yan ta'addan," inji Daramola. Ya ce an kai hare-haren ne a sumamen da aka kai a ranar Alhamis.

Daramola ya ce NAF tare da hadin gwiwa da sauran hukumomin tsaro za ta cigaba da yi wa 'yan ta'addan lugwuden wuta a yankin na Arewa maso Gabas domin tallafawa sojojin da ke aikin ragargazan 'yan ta'addan a kasa.

A cewarsa, ya ce Operation Rattle Snake da aka fara a ranar 4 ga watan Fabrairu an kafa shi ne domin tarwatsa sansanin 'yan ta'addan da ke arewa maso gabas domin taimakawa yaki da 'yan ta'addan.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164