Kyakyawar budurwa daga Yola za ta yi tattaki don haduwa da Sulen Garo

Kyakyawar budurwa daga Yola za ta yi tattaki don haduwa da Sulen Garo

Wata kyakyawar budurwa mai suna Honarabul Ameena Ameenu, ‘yar asalin birni Yola a jihar Adamawa ta bayyana cewa za ta yi tattaki zuwa jihar Kano don yin tozali da Murtala Sulen Garo.

Ameena Ameenu, ta sanar da hakan ne a shafinta na Facebook inda ta ce za ta yi tattakin ne a kafa don saduwa da kwamshinan kananan hukumomin na jihar kano.

Kamar yadda ta wallafa: “Assalamu alaikum, gaskiya ina ganin zan je Kano da kafa don neman Honarabul Murtala Sulen Garo, zan shirya yin tafiyar ne a ranar Laraba InshaaAllah.”

Wannan kuwa shine karo na farko da aka samu mace za ta yi wannan tattakin daga wata jihar zuwa wata domin taya murna ga wani dan siyasa.

Kyakyawar budurwa daga Yola za ta yi tattaki don haduwa da Sulen Garo
Kyakyawar budurwa daga Yola za ta yi tattaki don haduwa da Sulen Garo
Asali: Facebook

DUBA WANNAN: Sauya su Buratai: Fadar shugaban kasa ta bankado shirin masu cin moriyar kungiyar Boko Haram

Al’amarin yin tattakin dai ya zama ruwan dare a tsakanin matasa. Amma kuma masana a harkar siyasa na ganin irin hakan a abun da bai dace ba.

Ko a makon da ya gabata an samu wani saurayi da yayi tattaki daga Katsina inda ya je yi wa Gwamna Abdullahi Umar Ganduje murna a nasarar da ya samu a shari'ar da suka yi a kotun koli. Wannan saurayin kuwa ya samu tarba hannu bibbiyu daga hannun tawagar gwamnan bayan isarsa jihar Kano.

Ba wannan ba kadai aka yi a makon da ya gabata, wani saurayi yayi tattaki don zuwa yi wa Abba Gida-gida da Kwankwaso jajen shari'ar da aka yi a kotun kolin.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel