Forbes ta saki jerin masu kudin nahiyar Afrika, akwai yan Najeriya 4, 2 Kanawa ne (Kalli Jerin)

Forbes ta saki jerin masu kudin nahiyar Afrika, akwai yan Najeriya 4, 2 Kanawa ne (Kalli Jerin)

Hamshakin mai kudin Najeriya kuma Bakano, shugaban kamfanin Dangote Group, Alhaji Aliko Dangote, ne mutum mafi arziki a nahiyar Afrika a shekarar 2020. Rahoton Forbes.

Wannan shine karo na tara a jere da attajirin ya zarcewa dukkan masu halin nahiyar.

Jerin masu kudin ya mayar da hankali kan kasashen Afrika takwas masu kudi; yayinda kasar Masar da Afrika ta kudu suka da masu kudi biyar-biyar a jerin, Najeriya na da hudu, sannan kasar Maroko mai biyu.

Rahoton ya bayyana cewa Alhaji Aliko Dangote ya zo na daya da arzikin dala bilyan goma ($10.1 billion) na kasuwancinsa a Siminti, man fetur, flawa, Timatur da Sukari, sai Nassef Sawiris na kasar Masar mai arziki dala bilyan takwas ($8 billion) ya zo na biyu, sai Mike Adenuga mai kamfanin sadarwan Glo ya zo na uku.

Yan Najeriyan da suka shiga jerin masu kudin nahiyar sabanin Dangote sune Abdus Samad Isyaka Rabiu, Mike Adenuga, da Folorunsho Alakija.

Forbes ta saki jerin masu kudin nahiyar Afrika, akwai yan Najeriya 4, 2 Kanawa ne (Kalli Jerin)
Forbes ta saki jerin masu kudin nahiyar Afrika, akwai yan Najeriya 4, 2 Kanawa ne (Kalli Jerin)
Asali: Depositphotos

Ga jerin masu kudin nan:

Aliko Dangote $10.1 billion

Nassef Sawiris $8 billion

Mike Adenuga $7.7 billion

Nicky Oppenheimer $7.7 billion

Johann Rupert $6.5 billion

Issad Rebrab $4.4 billion

Mohamed Mansour $3.3 billion

Abdulsamad Rabiu $3.1 billion

Naguib Sawiris $3 billion

Patrice Motsepe $2.6 billion

Koos Bekker – $2.5 billion

Yasseen Mansour – $2.3 billion

Isabel dos Santos – $2.2 billion

Youssef Mansour – $1.9 billion

Aziz Akhannouch – $1.7 billion

Mohammed Dewji – $1.6 billion

Othman Benjelloun – $1.4 billion

Michiel Le Roux – $1.3 billion

Strive Masiyiwa – $1.1 billion

Folorunsho Alakija – $1 billion

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel