An kashe matashi dan kwallon kafa a gaban iyayenshi, lokacin da ake jana'izar kakanshi

An kashe matashi dan kwallon kafa a gaban iyayenshi, lokacin da ake jana'izar kakanshi

- An harbe wani matashin dalibi kuma dan kwallon kafa mai tasowa a wajen birne kakanshi

- Matashin mai shekaru 15, da zai je raka wasu ‘yan uwanshi ne wata kwaleji amma sai ya fasa don zuwa birne kakanshi

- Faston cocin ya ce yayi tsammanin za a yi rigima a wajen, shiyasa ya kawo jami’an tsaro amma suna tafiya abun ya faru

An harbe wani matashi a yayin bikin birne kakan shi. An gano cewa matashin yaron dan kwallon kafa ne mai tasowa kuma yana makarantar sakandire ne.

Terrance Jackson mai shekaru 15 ya mutu ne a ranar Asabar bayan da aka harbe shi. Wannan harbin kuwa shi ya hargitsa wajen makokin kakan shi da aka yi a Riviera Beach, in ji wata ‘yar sanda mai suna AJ Walker a ranar Litinin.

Royce Freeman mai shekaru 47 shima ya mutu a take. Wata mata kuwa ta samu rauni mai tarin yawa wanda ake gani a matsayin barazana ga rayuwarta.

Har yanzu dai ba a kama ko mutum daya ba amma Walker ta ce masu bincike na aikinsu.

Tronica da Terrance Jackson Sr. sun sanar da CBS Miami cewa su ganau ne ba jiyau ba a yadda mutuwar dansu ta zo.

KU KARANTA: Bankin FCMB ya dauki nauyin karatun dalibar da take rubuta jarrabawa a gaban bankin da daddare

“A lokacin da na isa wajenshi, nayi kokarin cire mishi botirin wuyan rigar shi, ina kuma ce mishi yayi numfashi. Ya girgiza kanshi amma a haka ya ciki.” Cewar Tronica.

Terrance Jackson Sr. ya ce: “A lokacin kawai dukkan rayuwar shi ce ta dawo min. Na tuna lokacin da aka haifeshi a gabaan ya fara numfashi amma sai gashi a gabana numfashin shi ya dauke.”

Jackson wanda aka fi kira da Teejay, ya kamata a ce ya raka wasu ‘yan uwan shi 20 ne zuwa wata tafiya amma sai ya tsaya don birne kakanshi.

An fara harbin ne da rana a tsallaken titin cocin Victory, inda ake birne kakan nashi. Faston cocin mai suna Tywuante D. Lupoe ya sanar a wani bidiyo da ya wallafa a Facebook.

Ya kara da cewa sun san akwai yuwuwar a yi tashin hankali don haka ne suka kawo jami’an tsaro. Jami’an tsaron sun tafi kenan aka fara harbin.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng