Yanzu-yanzu: Bam ya tashi a gidan gwamnatin jihar Ekiti

Yanzu-yanzu: Bam ya tashi a gidan gwamnatin jihar Ekiti

Tashin hankali da hargitsi ya mamaye yankin Okesha na jihar Ekiti a yau ranar Asabar bayan da bam ya tashi a kusa da tsohon gidan gwamnatin jihar.

Jaridar The Cable ta gano cewa tashin bam din yayi sanadiyyar tarwatsewar wasu gine-gine a yankin. Kuma hakan ya shafi wani bangare na ma'aikatar masarautun jihar.

Tashin bam din ya kawo tarwatsewar wani bangare na ma'aikatar kudi da sauran gine-ginen da ke farfajiyar.

Yanzu-yanzu: Bam ya tashi a gidan gwamnatin jihar Ekiti
Yanzu-yanzu: Bam ya tashi a gidan gwamnatin jihar Ekiti
Asali: UGC

Amba Asuquo, kwamishinan 'yan sandan jihar ya hallara a inda abin ya faru. Ya ce an fara binciken farko don gano sanadin fashewar bam din a farfajiyar.

DUBA WANNAN: Faduwa zabe: Abdulmumin Kofa ya mayarwa majalisa dukiyoyinta

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Tags:
Online view pixel