Rashin tsaro: Akalla mutane 245 aka kashe a watan Junairu (Duba jerin wadanda aka kashe)

Rashin tsaro: Akalla mutane 245 aka kashe a watan Junairu (Duba jerin wadanda aka kashe)

Akalla mutane 245 suka rasa rayukansu a watan farkon shekarar 2020, rahotannin kashe-kashe da aka tattara ya bayyana hakan.

A cewar rahoton bincike da InterNations ta gudanar, Najeriya ce kasa mafi hadarin zama a duniya na uku bayan kasar Afghanistan da Syriya.

Ga jerin yadda kashe -kashen suka auku a watan Junairu:

2 ga Junairu: Sojojin Najeriya sun kashe yan Boko Haram 8 yayinda sukayi kokarin kai hari Michika, jihar Adamawa

4 ga Junairu: Wasu yan bindiga sun hallaka mutane 23 a garin Tawari, a jihar Kogi

6 ga Junairu: Akalla mutane 30 suka hallaka yayinda Bam ta tashi da su kan gada a Gamboru, jihar Borno

Hakazalika a ranar, an hallaka jami'an Sojin ruwa hudu yayinda akayi garkuwa da turawa uku a Neja Delta.

Kuma dai a ranar, an hallaka Sojoji hudu a kauyen Gwarm, karamar hukumar Munya ta jihar Neja.

7 ga Junairu: Wani dan sanda a Yenegoa, jihar Bayelsa ya hallaka mutane uku: Direba, mai bautan kasa, da wani mutum daya.

Hakazalika a ranar, fusatattun matasa sun babbaka wasu barayi biyu da suka kai hari shagon aski yayinda wasu bindiga kuma suna kashe wani Yasir Umar a jihar Katsina.

9 ga Junairu: Hukumar yan sandan jihar Plateau ta tabbatar da kisan mutane 12 a kauyen Kulben, karamar hukumar Mangu ta jihar.

11 ga Junairu: Yan bindgia sun bindige jami'an Sojin sama hudu a hanyar Birnin Gwari, jihar Kaduna.

14 ga Junairu: Rikici tsakanin manoma da makiyaya ya haddasa kisan mutane biyu a garin Sobe, karamar hukumar Owan ta jihar Edo.

Hakazalika a ranar, an hallaka Sojin ruwa 4 a kauyen Gbagira, karamar hukumar Ilaje ta jihar Ondo.

16 ga Junairu: Wasu yan bindiga sun kai hari karamar hukumar Gummi a jihar Zamfara inda suka hallaka akalla mutane 23.

A ranar kuma, yan bindiga suka kaiwa sarkin Potiskum, Alhaji Umaru Bubaram, harin kwantan bauna a hanyar Kaduna zuwa Zariya inda suka kashe akalla mutane 6.

18 ga Junairu: An hallaka Soja daya da Boko Haram hudu a musayar wutan da akayi a Ngala, yayinda aka kashe yan gudun hijra akalla 20.

Hakazalika ranar yan Boko Haram suka kashe Sojoji 4 a Bama.

A ranar dai, rikicin kabila ya barke a karamar hukumar Igalamela-Odolu a jihar Kogi kuma akalla mutane 4 sun hallaka.

19 ga Junairu: Gobara ta hallaka mutane biyar yayinda Barayin mai suka fasa bututu mai a jihar Legas

Hakazalika a ranar, bidiyo ya bayyana inda wani dan karamin yaro na Boko Haram ya kashe wani dalibi

20 ga Junairu: An hallaka akalla Sojoji 17 yayinda akayi garkuwa da dama cikinsu a artabun da ya auku tsakanin Soji da Boko Haram kan hanyar Bama-Gwoza.

21 ga Junairu: An hallaka Sojoji 8 a musayar wuta da Boko Haram a Kaga, jihar Borno.

Yan bindiga sun hallaka mutane 4 a karamar hukumar Keana a jihar Nasarawa, yan Boko Haram sun hallaka shugaban CAN, Lawal Andimi, kuma yan bindiga suka kashe muyane 14 a Batsari jihar Katsina.

23 ga Junairu: Yan Boko Haram sun hallaka mutane 10 a Dikwa.

24 ga Junairu: Fusatattun matasa sun hallaka barayi biyu a karamar hukumar Yenagoa, jihar Bayesla.

25 ga Junairu: Yan kunar bakin wake sun tayar da Bam a Masallaci a garin Gwoza, jihar Borno. Mutane 3 suka hallaka yayinda da yawa suka jikkata.

Hakazalika a ranar, yan bindiga sun hallaka mutane mutane 13 a Kwatas, karamar hukumar Bokkos jihar Plateau yayinda yan bindiga suka kashe mutane 11 a jihar Neja.

27 a Junairu: Wani matashi ya burmawa budurwarsa wuka har lahira saboda ta amsa wayan wani saurayi

29 ga watan Junairu: Wani mutum mai suna Kalu ilum ya bindige matarsa, a Etitiama Nkporo dake Ohafia jihar Abia. Sai matasan gari suka banka masa wuta.

Hakazalika wasu makiyaya sun kashe muaten 2 a karamar hukumar Ovia ta Arewa a jihar Edo.

30 ga Junairu: Yanfashi sun hallaka wani dan bautan kasa, Adebayo Mukaila, a jihar Osun

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng