Da duminsa: Alhassan Ado Doguwa ya sake lashe zabe

Da duminsa: Alhassan Ado Doguwa ya sake lashe zabe

Hukumar gudanar da zabe ta kasa INEC ta alanta Alhassan Ado Doguwa, matsayin zakaran zaben mai-mai na mai wakilatan mazabar Tudun Wada/Doguwa a majalisar wakilan tarayya.

Baturen zaben, Farfesa Mansur Bindawa, ya bayyana cewa Ado Doguwa na jam'iyyar All Progressives Congress, APC, ya samu kuri'u 66,667 yayinda abokin hamayyarsa Yusha’u Salisu na jam'iyyar Peoples Democratic Party, PDP ya samu kuri'u 6,323 .

Za ku tuna cewa a ranar 4 ga Nuwamba, 2019, kotun daukaka kara dake zauna a Kaduna ta fitittiki Ado Doguwa wanda yake shugaban masu rinjaye a majalisar, tun ta bada umurnin sabon lale.

Da duminsa: Alhassan Ado Doguwa ya sake lashe zabe
Da duminsa: Alhassan Ado Doguwa ya sake lashe zabe
Asali: Facebook

Mun kawo muku rahoton cewa Tsohon dan majalisan wakilan tarayya, AbdulMumini Jibrin, ya fadi ba nauyi a zaben mai-mai da aka gudanar a mazabar Kiru/Bebeji na jihar Kano.

Jibrin wanda yake dan jam'iyyar All Progressives Congress (APC) ya sha kasa hannun abokin hamayyarsa Alhaji Ali Datti Yako, na Peoples Democratic Party (PDP) da aka gudanar 25 ga Junairu, 2020.

Baturen zaben, Farfesa Abdullahi Arabi, ya ce Ali Datti ya samu kuri'u 48,641 yayinda AbdulMumini Jibrin ya samu kuri'u 13,507.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel