Amotekun: An yiwa furucina bahaguwar fahimta ne - Malami

Amotekun: An yiwa furucina bahaguwar fahimta ne - Malami

- Abubakar Malami (SAN) a ranar Alhamis, 23 ga watan Janairu ya soke furucinsa na farko game da billowar kayan tsaro na kudancin Najeriya wanda ya ce ba ya bisa oka

- Malami ya yi ikirarin cewa gwamnonin kudu maso yamma da mutanen kudancin Najeriya be suka yiwa kalamin nasa wata fassara na daban

- Ya bayyana hakan ne a hira da gidan radiyo na Najeriya a Abuja

Atoni janar na tarayya kuma ministan shari’a, Abubakar Malami (SAN) a ranar Alhamis, 23 ga watan Janairu ya soke furucinsa na farko game da billowar kayan tsaro na kudancin Najeriya wanda ya kaddamar a matsayin ba bisa ka’ida ba.

Malami wanda sukar kayan Operation Amotekun da ya yi ya haifar da cece-kuce a shafukan sadarwa ya yi ikirarin cewa gwamnonin kudu maso yamma da mutanen kudancin Najeriya be suka yiwa kalamin nasa wata fassara na daban.

KU KARANTA KUMA: Abdulmumin Jibrin ya saduda, yana neman sulhu da shugabannin APC gabannin zaben da za a sake (bidiyo)

Atoni Janar din wanda ya yi wannan jawabin a wata hira da gidan radiyo na Najeriya a Abuja a safiya yau Alhamis ya ce “an yiwa furucina kan Operation Amotekun wata fassara ne na daban, ban ce baya bisa doka ba.”

A baya mun ji cewa Sakataren kungiyar Afenifere na kasa, Kole Omololu, ya caccaki jagaban Bola Tinubu a kan matsayarsa a sabon salon tsaro da aka kirkiro a yankin Kudu maso yamma mai suna Amotekun.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng