Buhari ya sabunta nadin mutane 2 dake bashi shawara a kan lamuran gajiyayyu

Buhari ya sabunta nadin mutane 2 dake bashi shawara a kan lamuran gajiyayyu

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya sake nada Samuel Ankeli a matsayin babban mataimaki na musamman (SSA) a kan lamuran gajiyayyu.

Ya kara nada Malam Garba Shehu a matsayin mataimaki na musamman (SA) a kan lamurra gajiyayyu.

Nadin ya fara aiki ne daga ranar 15 ga watan Oktoba 2019, kamar yadda takardar da Garba Shehu, babban mataimaki na musamman ga shugaba Buhari a kan yada labarai ya fitar.

An fara nada hadiman na musamman din ne tun lokacin da shugaban kasar ya fara hawa mulkin kasar a karo na farko.

A wani labari na daban, Makaddashin shugaban hukumar yaki da cin hanci da karya tattalin arzikin kasa, Ibrahim Magu, ya bayyana cewa hukumarsa zata nemi a dawo da duk wasu mabarbata dukiyar jama'ar Najeriya da suka turai suka buya.

DUBA WANNAN: Zamu dawo da duk mabarnatan da suka gudu turai suka buya - Magu

Shugaban na EFCC ya bayyana hakan ne ranar Talata yayin da yake gana wa da manema labarai a ofishin shiyyar hukumar na Ilorin.

Magu, wanda ya kai ziyarar aiki jihar Kwara, ya bayyana cewa an shigo sabuwar shekara, a saboda haka hukumar EFCC ta sabunta yakin da take yi da karya tattalin arziki kuma za a gurfanar da duk wanda aka samu da laifi.

"Zamu gayyaci da duk wanda muke bincike, sannan mu gurfanar da shi a gaban kotu da zarar mun kammala bincike. Wannan somin tabi ne, zamu nemi a dawo da mabarnata da dama da suka gudu turai suka buya, basu tsira ba don kawai suna zaune a kasashen ketare. Tamkar yanzu muka fara yaki da cin hanci, mun fito da karfinmu a sabuwar shekaru," a cewar Magu.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng