Yanzu-yanzu: Na yi tafiya a kafa na sa'o'i biyu bayan harin Boko Haram - Sarkin Potiskum

Yanzu-yanzu: Na yi tafiya a kafa na sa'o'i biyu bayan harin Boko Haram - Sarkin Potiskum

Sarkin Potiskum, Mai martaba Alhaji Umaru Bubaram Ibn Wuriwa Bauya ya yi magana a kan harin da 'yan ta'addan kungiyar Boko Haram suka kai masa inda hudu daga cikin hadimansa suka rasa rayyukansu a ranar Talata.

Ya ce ya yi tafiya a kafa na kimanin sa'o'i biyu a cikin daji domin ya tsira da ransa yayin harin da 'yan ta'addan suka kai wa tawagarsa a kan hayar Kaduna zuwa Zaria.

Sarkin ya mika godiyarsa ga Allah da ya kubutar da shi da sauran hadimansa daga harin bayan ya koma fadarsa a Potiskum na jihar Yobe daga asibiti a Kaduna inda aka kai shi likitoci suka duba shi.

DUBA WANNAN: Safarar yara: 'Yan sanda sun kama Farfesa a Kano

Sai dai duk da haka sarkin ya yi bakin cikin rasuwar hudu daga cikin hadimansa tare da daya da har yanzu ba a san inda ya ke ba.

Sarkin da ya yi magana da wakilin The Nation a fadarsa da ke Potiskum ya yi kira da dukkan mutane su goyi bayan gwamnatin tarayya don samar tsaro a kasar.

Ku biyo mu don karin bayani ...

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164