Hotunan ziyarar da Ahmed Musa da 'yan kungiyarsa suka kai wa yariman Saudiyya

Hotunan ziyarar da Ahmed Musa da 'yan kungiyarsa suka kai wa yariman Saudiyya

Kyaftin din Super Eagles Ahmed Musa tare da sauran tawagarsa na Al Nassr sun kai wa yariman Saudiyya, Faisal Bin Bandar Al Saud ziyarar ban girma bayan sunyi nasarar lashe Saudi Super Cup.

Musa da 'yan tawagarsa sun doke Al Taawon da 5 -4 a bugun daga kai sai mai tsaron gida a filin wasa na Sarki Abdullah da hakan ne suka samun nasarar zama zakarun gasar kwararru na Saudiyya kamar yadda Today.ng ta ruwaito.

A yayin da suke cigaba da murnar samun nasarar zama zakarun gasar a karo na farko, tawagar sun kai wa yariman ziyarar ban girma don godiya bisa goyon bayan da ya ke basu kasancewa yana daya daga cikin masu goyon bayan kungiyar.

DUBA WANNAN: Kano: Da haramtattun kuri'u aka zabi Ganduje - Abba Gida-Gida

Wannan shine kofi na biyu da kungiyar ta zama zakara a gasar cin kofi tun bayan da Musa ya baro Leicester City ya dawo kungiyar ta yankin Larabawa.

Kungiyar ta wallafa hotunan ziyarar da suka kai wa yariman na Saudiyya a kafafen sada zumunta da suka yi wa lakabi da "Mai martaba, Yariman Saudiyya Faisal bin Bandar Al Saudi, gwamnan Riyadh ya karbi bakuncin zakarun #SaudiSuperCup."

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164