Rashin tabbas a Afirka: Dangote zai bude sabon ofis a Amurka

Rashin tabbas a Afirka: Dangote zai bude sabon ofis a Amurka

Attajirin dan kasuwa, Aliko Dangote ya ce zai bude sabuwar ofishi a birnin New York na Amurka domin ya rararraba hannun jarinsa don kaucewa hauhawa da sakan naira a Najeriya.

Da ake hira da shi a wani shiri mai suna Rubenstein Show a Bloomberg TV, Dangote ya ce, "Ka san cewa a Afirka muna da matsalar rage darajar kudadenmu, saboda haka muna son mu adana wasu daga cikin dukiyar mu."

Dama attajirin na Afirka kuma mutum mafi arziki a duniya na 95 yana da ofishi a birnin London.

Duk da cewa yana da kamfanoni biyar, a halin yanzu ba a san ko wane cikinsu zai bude mata reshe a New York ba.

Attajirin mai dan shekara 63 ya samu karin arziki na biliyan 4.3 a 2019 sakamakon saka jarin da ya yi a samar da siminti, flawa da sukari. Da zarar an kammala matatan man fetur din da ya ke ginawa wa arzikinsa zai kara bunkasa.

DUBA WANNAN: Albashi na duk wata N54 ne a matsayin malamin makaranta - Sanata Wamakko

Ana sa ran matatar zai rika samar da gangan man fetur 650,000 a duk rana.

Matatar man zai wadatar da 'yan Najeriya baki daya duba da cewa a yanzu kasar tana shigo da tattacen man fetur ne daga kasashen waje domin biyan bukatunsu.

Dangote kuma yana gina masana'antar sarrafa takin zamani a wurin.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164