Allah mai iko: Likitoci sun samu nasarar raba wasu yara da aka haifesu a hade, bayan shafe awa 13 suna tiyata

Allah mai iko: Likitoci sun samu nasarar raba wasu yara da aka haifesu a hade, bayan shafe awa 13 suna tiyata

- Wasu tagwaye da aka haifa a manne da juna sun fara rayuwa a rabe

- Gwamnatin tarayya ce ta dauki nauyin raba su, inda kwararru suka yi musu aiki a asibitin kasa dake Abuja

- Ministan lafiya, Dr Osagie ya jinjinawa kungiyar kwararrun likitocin da suka yi aikin

Wasu tagwaye da aka haifa a manne da juna sun fara rayuwa a rabe bayan wata kungiyar kwararrun likitoci suka dau sa'o'i 13 suna aikin raba su a Abuja, babban birnin kasar nan.

Goodness da Mercy sun zo a ba-zata da aka haifesu a ranar 13 ga watan Augusta a babban asibitin tarayya dake Keffi a jihar Nasarawa. An haifesu ne ta hanyar yiwa mahaifiyarsu aiki duk da kuwa bata san tana dauke da tagwaye bane. Bayan fito dasu ne aka ga kirjinsu da cikinsu a hade.

An bukaci kusan naira miliyan 20 don yi musu aikin da zasu rabe tun bayan hadewarsu a cikin mahaifa.

Abun farin cikin ya fara ne a lokacin da babban asibitin kasa dake Abuja suka yanke hukuncin yi musu aikin a kyauta. Hakan ne kuwa yayi sanadin aikin da ya raba manannun tagwayen.

A ranar Talata da ministan ilimi ya gabatar da jawabi na musamman a kan rabe tagwayen, Dr Osagie Ehanire ya danganta nasarar wannan aikin da goyon bayan hadaka daga kwararrun da kuma gwamnatin tarayyar da ta dauki nauyi.

KU KARANTA: San barka: Jaruma Rahama Sadau ta kafa gidauniya don samawa almajirai kayan sanyi

Ya ce: "Wadannan kyawawan jariran 'yan asalin jihar Benuwe ne kuma muna matukar alfahari da iyayensu.

"Kungiyar kwararrun da aka ba wannan aikin sun nuna kwarewarsu a fannin lafiya duk da matsakaitan kayan aikin da ake dasu. A hakan kuwa muna da tabbacin cewa zamu kai kololuwa a fannin kiwon lafiya a duniya."

Tun bayan da suka sauka a Abuja, anyi wa tagwayen aiki har sau hudu a bangarori daban-daban na lafiya. Sunyi kuma watanni 16 suna karbar kulawar kwararrun masana a kiwon lafiya.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng