Jerin Coci-coci 10 da aka mayar Masallatai a duniya

Jerin Coci-coci 10 da aka mayar Masallatai a duniya

Daya daga cikin wasiyyar karshe da manzon Allah (SAW) ya yi shine haramta wariyar launin fata da asabiyyanci inda yace: Dukkanmu daga Annabi Adam muke, kuma Annabi Adam daga tabo aka halliceshi.

Shiyasa yawaitan Musulmai a kasashen Turai da Amurka bai zama abin mamaki ba inda bincike ya nuna cewa nan da shekarar 2040, yawan Musulmai zai zarcewa Kirista a duniya.

A yanzu haka, akwai cocina da dama daka sauya zuwa Masallatai a wasu sassan duniya musamman Amurka.

Ga jerin Masallatan:

1. Cocin Katolikan St Gerard dake New York, Amurka: An sauyan cocin zuwa Masallaci ne bayan kotu ta bada umurnin haka saboda yawaitan adadin Musulmai a birnin New York.

2. Cocin St. Nicholas: An mayar da cocin Masallaci ne a shekarar 1968 bayan gwamnatin kwaminisanci ta rusashi

3.Cocin Hagia Sopia: An sauya zuwa Masallaci ne bayan gwamnatin Ottoman ya kwace mulki a Anatoliya, Turkiyya

4.Cocin Katolikan St Philip: Asalinta Masallaci ce amma aka mayar Coci a shekarar 1845 kafin aka sake mayar da ita Masallaci a 1962

5.Masjid Isa Ibn Maryam dake Syracuse, New York asali cocin Katolika ne

DUBA NAN: An sace N16m na albashin mutane a ofishin sakataren gwamnatin jihar Katsina

6.Jami Masjid in Buffalo, New-York, asali cocin Katolika ne

7.Babban Masallacin Tangiers dake Morocco asalin Cocine

8. Cocin St Anthanasiuis: Asali cocin Katolika ne aka mayar Masallaci lokacin da addinin Musulunci ya shiga kasar Masar

9.Cocin Jamus da aka mayar Masallaci domin masallata 2000

10.Masallacin Nyalgosi Jamia: Asalin sunansa Cocin Nyalgosi ne a Kenya. An mayar da ita Masallaci ne bayan Faston ya karbi addinin Musulunci.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng