Abun al’ajabi: Wani katoton karfe ya rufto daga sararin samaniya a Nijar

Abun al’ajabi: Wani katoton karfe ya rufto daga sararin samaniya a Nijar

Rahotanni sun kawo cewa wani katoton karfe ya fado daga can saurarin samaniya, inda ya sauka a wani kauye da ke garin Tania a yankin Damagaram na kasar Nijar.

An tattaro cewa faruwar wannan lamari ya girgiza mazauna yankin.

A cewar mazauna yankin, sun ji kara mai tsoratarwa tare da ganin gilmawar hasken walkiya jim kadan bayan fadowar karfe a kauyen Tazai.

An rahoto cewa lamarin ya afku ne a ranar 31 ga watan Disamba ta 2019.

Tuni dai gwamnatin Nijar ta tura wata tawaga ta kwararru d hukumomi da jami’an tsaro zuwa yankin don ganin abunda ya faru.

KU KARANTA KUMA: Tanko Yakasai ya caccaki Buhari da APC, ya ce babu abunda ya chanja a Najeriya tun 2015

Daraktan hukumar ma’adinai ta kasar a Damagaram, Na Allah Ousmane, ya tabbatar da faruwar lamarin inda ya ce, a halin da ake ciki wasu kwararru na musamman na gudanar da bincike kan karfen wanda a cewarsa yana da nauyi sosai.

A wani labari na daban, mun ji cewa akalla mutane 30 ne suka mutu a jihar Borno bayan tashin wani bam da aka dana a kan wata gada, majiyoyi suka fada ma Reuters a ranar Litinin.

Bam din ya tashi ne da misalin karfe 5:00 na yamma a gadar da ke cike da mutane a kasuwar garin Gamboru da ya shiga har kasar Kamaru.

Idanun shaida a kasuwar sun ce an kai sama da mutane 35 da suka jikkata zuwa asibiti biyo bayan harin.

Idan ku na da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewa tare da mu.

Asali: Legit.ng

Online view pixel