Abun al’ajabi: Wani katoton karfe ya rufto daga sararin samaniya a Nijar

Abun al’ajabi: Wani katoton karfe ya rufto daga sararin samaniya a Nijar

Rahotanni sun kawo cewa wani katoton karfe ya fado daga can saurarin samaniya, inda ya sauka a wani kauye da ke garin Tania a yankin Damagaram na kasar Nijar.

An tattaro cewa faruwar wannan lamari ya girgiza mazauna yankin.

A cewar mazauna yankin, sun ji kara mai tsoratarwa tare da ganin gilmawar hasken walkiya jim kadan bayan fadowar karfe a kauyen Tazai.

An rahoto cewa lamarin ya afku ne a ranar 31 ga watan Disamba ta 2019.

Tuni dai gwamnatin Nijar ta tura wata tawaga ta kwararru d hukumomi da jami’an tsaro zuwa yankin don ganin abunda ya faru.

KU KARANTA KUMA: Tanko Yakasai ya caccaki Buhari da APC, ya ce babu abunda ya chanja a Najeriya tun 2015

Daraktan hukumar ma’adinai ta kasar a Damagaram, Na Allah Ousmane, ya tabbatar da faruwar lamarin inda ya ce, a halin da ake ciki wasu kwararru na musamman na gudanar da bincike kan karfen wanda a cewarsa yana da nauyi sosai.

A wani labari na daban, mun ji cewa akalla mutane 30 ne suka mutu a jihar Borno bayan tashin wani bam da aka dana a kan wata gada, majiyoyi suka fada ma Reuters a ranar Litinin.

Bam din ya tashi ne da misalin karfe 5:00 na yamma a gadar da ke cike da mutane a kasuwar garin Gamboru da ya shiga har kasar Kamaru.

Idanun shaida a kasuwar sun ce an kai sama da mutane 35 da suka jikkata zuwa asibiti biyo bayan harin.

Idan ku na da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewa tare da mu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng