Musabaqar Al-Kur'ani mai girma: Jihar Kaduna da Kano sun ciri tuta a gasar bana
Umar Kabir daga jihar Kaduna da Diya’atu Sanni Abdulkadir daga jihar Kano sun zama gwarazan shekara a gasar Musabaqar Al-Kur'ani kasa karo na 34 da aka kammala yau Asabar, 4 ga watan Junairu, 2020 a jihar Legas.
Gasar karatun Al-Kur'anin da gidauniyar Musabaqah Al-Kur'ani tare da cibiyar ilmin addinin Musulunci dake jami'ar Usmanu Danfodiyo Sokoto suka shirya ya kaddama ranar Juma'ar da ta gabata inda mai alfarma sarkin Musulmai ya bude.
Hazikan mahaddata Al-Qur'ani maza da mata, yara da manya daga jihohin Najeriya 36 sun yi musharaka a Musabaqar a bangarorin daban-daban.
Bangarorin sun da hada Hizbi 60 da tafsiri, Hizbi 60 babu tafisri, Hizbi 40, Hizbi 20, Hizbi 10, da Hizbi 2.
Bayan kwashe mako daya ana fafatawa, an sanar da sakamakon gasar na bangarorin daban-daban.
Ga yadda sakamakon ya kasance:
Hizbi 2 (Maza)
3-Kaduna
2- Anambra
1- Lagos
Hizbi 2 (Mata)
3- Abuja
2- Lagos
1- Kaduna
Hizbi 10 (Maza)
3- Borno
2- Zamfara
1- Kano
Hizbi 10 (Mata)
3- Lagos
2- taraba
1- Gombe
Hizbi 20 (Maza)
3- Borno
2- Adamawa
1- Bauchi
Hizbi 20 (Mata)
3- Plateau
2- kwara
1- Borno
Hizbi 40 (Maza)
3- Kaduna
2- Plateau
1- Jigawa
Hizbi 40 (Mata)
3- Kaduna
2- Adamawa
1- fct Abuja
Hizbi 60 (Maza)
3- Borno
2- Gombe
1- Kaduna
Hizbi 40 (Mata)
3- Adamawa
2- fct Abuja
1- Zamfara
Hizbi 60 da Tafsiri (Maza)
3- Zamfara
2- Niger
1-Kaduna ( Gwarzon shekara)
Hizbi 60 da Tafsiri (Mata)
3- Zamfara
2-Katsina
1-Kano ( Gwarzuwar shekara)
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng