An kaiwa Gwamna Oyetola da matarsa hari a taron murnar sabon shekara

An kaiwa Gwamna Oyetola da matarsa hari a taron murnar sabon shekara

- Wasu bata gari sun kai wa hari gwamnan jihar Ogun da tawagarsa a jajiberin sabuwar shekara

- Bata garin sun jefi gwamnan ne, matarsa da shugaban ma'aikatan jihar a filin wasa na Nelson Mandela da ke Osogbo

- A halin yanzu dai mutum daya ya shiga hannu, baya da aka gane yana da sa hannu a cikin wannan tada zaune tsayen

Wasu bata gari sun kaiwa gwamnan jihar Osun, Adegboyega Oyetola da wasu mukarrabansa hari a sa’o’in farko na ranar Laraba a yayin taron fara murnar sabuwar shekara a gidan gwamnatin jihar dake Osogbo.

Wannan taron da aka fara a filin yanci na Nelson Mandela ya tashi ne babu dadi wajen karfe 1 na dare, yayin da wasu mutane suka fara jifan ida manyan bakin, gwamnan, matarsa da shugaban ma’aikatan jihar ke zaune kamar yadda The Punch ta ruwaito.

DUBA WANNAN: Yadda wata amarya ta daure fuska a hoton auren ta ya dauki hankalin mutane

Wani mutum daya da ba a tabbatar da sunansa ba a yayin rubuta wannan rahoton, ya shiga hannu saboda an gano yana da hannu a cikin wannan tashin-tashinar da karantsaye ga zaman lafiya.

Daga cikin manyan bakin dake wajen akwai shugaban jam’iyyar APC na jihar, Gboyega Famoodun; sakataren gwamnatin jihar, Wole Oyebamiji; da kwamishinan aiyuka na musamman, Lekan Badmus.

Kafin faruwar al’amarin, an saka kida na wakokin zamani kuma mawakan zamanin suna ta baje kolinsu da nuna bajintarsu a fili. Ana kuma bada kyautuka ga mutane.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164