Rundunar soji ta bayyana dalilin da yasa motar yakinta ya babbake a Damaturu

Rundunar soji ta bayyana dalilin da yasa motar yakinta ya babbake a Damaturu

Rundunar sojojin Najeriya a ranar Talata, 31 ga watan Nuwamba, ta ce matsalar na’urar lantarki ne ya haddasa fashewar motar yakinta a Damaturu, jihar Yobe a ranar Litinin.

Tarwatsewar motar da wutar da ke ta tashi ya haifar da tashin hankali a birnin. Sojoji uku sun ji raunuka da dama a yanayin.

Kyaftin Njoka Irabor, mataimakin daraktan hulda da jama'a na rundunar sashi 2, na Operation Lafiya olee ya bayyana hakan a wani jawabi. jawabin ya zo kamar haka: "An samu tashin hankali a garin Damaturu sakamakon karar fashewar wasu abubuwa a ranar Litinin, 30 ga watan Disamba. "Lamarin tashin wutan ya afku ne lokacin da wata motar yaki ke a hanyar komawa sansani aga wani aiki, sai wani waya ya samu matsala.

"Wannan ya yi sanadiyar babbakewar motar sannan ya kama da wuta.

"Lamarin ya afku ne a hanyar Damaturu zuwa Maiduguri. "Motar ya babbake baki daya, yayinda dakarun da ke motar suka yi nasarar fitar da kansu a tashin wutar.

"Sai dai sojoji uku sun ji rauni sannan tuni aka kai su cibiyar lafiya domin samun kulawar likitoci.

KU KARANTA KUMA: Rundunar sojin Najeriya za ta janye dakarunta daga arewa maso gabas

"Sannan, Hedkwatar sashi na 2 na Operation Lafiya DDole, na fatan amfani da wannan damar don bukatar mazauna Damaturu da kewayensu a su tafi harkokin gabansu, domin dakarunmu za su cigaba da aiwatar da ayyukansu domin kare rayuka da dukiyoyi."

Idan ku na da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewa tare da mu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng