Kano: Sarkin Karaye ya sauke manyan hakimai guda 2 a karkashin masarautarsa

Kano: Sarkin Karaye ya sauke manyan hakimai guda 2 a karkashin masarautarsa

- Majalisar masarautar Karaye ta kwace rawunan hakiman Kiru da Rimin-Gado na yankin

- Hakan ya biyo bayan zargar hakiman da aka yi da laifin rashin biyayya da cin amana

- Tuni masarautar ta zabi wasu hakiman don maye gurbin wadanda ta sauke

Majalisar masarautar Karaye ta jihar Kano ta kwace rawunan hikimin Kiru, Alhaji Ibrahim Hamza da na hakimin Rimin-Gado, Alhaji Shehu Muhammad a kan zarginsu da take da cin amana.

Majalisar masarautar ta yanke wannan hukuncin ne bayan zamanta na biyo wanda ya samu shugabanci Sarkin Karaye, Dr. Ibrahim Abubakar II a fadar masarautarsa da ke Karaye.

Wannan na kunshe ne a takardar da jami’in yada labarai na masarautar Karaye, Alhaji Haruna Gunduwawa ya fitar a ranar Lahadi a jihar Kano.

DUBA WANNAN: Asibiti: 'Yan fashi da makami sun yi wa majinyata da ma'aikatan asibiti fashi

“Majalisar masarautar ta amince da nada Alhaji Auwalu Ahmad a matsayin hakimin Rimin-Gado, Magajin Rafin Karaye, a matsayin hakimin Kiru da kuma Alhaji Garba Alhaji a matsayin Dan Madamin Karaye,” in ji shi.

Gunduwawa ya ce, majalisar ta amince da nadin Malam Shehu Ahmed a matsayin hakimin Karaye.

“Majalisar tana taya sabbin hakiman murna tare da musu addu’ar Allah ya sha gabansu a yayin sauke nauyinsu. Taron ya samu halartar shuwagabannin kananan hukumomin da ke karkashin masarautar da sauran ‘yan majalisar.” Cewar Gunduwawa.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng

Tags: