Jerin matan arewa guda 5 da suka yi fice wajen kare hakkin Dan Adam a duniya
- An ware kowacce ranar 10 ga watan Disamba ta shekara don bikin kare hakkin dan Adam
- Fafutukar kare hakkin mata kuwa na daga cikin hakkokin dan Adam
- Akwai mata masu tsananin gwarzanta da suka taka rawar gani wajen kare hakkin mata a arewacin Najeriya
A kowacce ranar 10 ga watan Disamba ne ake bikin kare kare hakkin dan Adam. An amince da ranar ne tun a shekarar 1948. Akwai mata masu yawa da ke fafutukar kare hakkin mata. Ga mata biyar da suka yi fice a wajen kare hakkin dan Adam a arewacin Najeriya.
1. Laila Dogonyaro

Asali: Facebook
Haifaffiyar birnin Kano ce a 1944. An yi mata aure tana da shekaru 13 a duniya. Ta rasu tana da shekaru 66 a shekarar 2011.
Hajiya Laila ta shahara wajen fafutukar kare hakkin mata, musamman ganin an ilimantar da su.
Ta shugabanci kungiyoyin mata daban-daban. Kafin nan kuwa, tana cikin matan da suka kirkiri jam'iyyar matan Arewa da nufin taimaka wa iyalai matalauta a arewacin Najeriya.
2. Hafsat Baba

Asali: Facebook
An haife ta ne a 1957 kuma ta shahara wajen fafutukar kare hakkin mata wadanda suka rasa mazajensu da kananan yara, musamman marayu.
Ta yi kwamishinar kula da ayyukan jin kai da walwalar al'umma a jihar Kaduna. Kafin nan, ta rike mukamin kwamishinar mata.
3. Saudatu Mahadi

Asali: Facebook
Mace ce mai fafutukar kare hakkin mata da kwato 'yancinsu a Najeriya.
Ta taba zama mamba a majalisar gudanarwa ta hukumar kare hakkin dan Adam a Najeriya. Tana daga cikin matan da suka assasa yekuwar Bring Back Our Girls da nufin zaburar da hukumoni don ceto 'yan matan Chibok.
4. Maryam Awaisu

Asali: Facebook
Marubuciya ce kuma mai fafutukar kare hakkin mata. Tana daga cikin matasan mata da suka assasa yekuwar #ArewaMeToo. Kungiyar na karfafa guiwar wadanda aka taba yi wa fyade su fito su fada don a dauki mataki.
5. Hassana Maina

Asali: Facebook
Ta karanci aikin lauya a jami'ar Ahmadu Bello ta Zaria. Matashiyar mai shekaru 21 da haihuwa jigo ce a fafutukar #NorthNormal. Kungiyar na da burin ganin jihohin Najeriya sun haramta cin zarafin jama'a a cikin kundin dokokinsu.
A yanzu haka, tana jagorantar wani shiri na wayar da kan yara 'yan makaranta game da cin zarafi ta hanyar lalata.
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu:
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng