Abubuwa 8 da ya kamata ku sani game da sabon shugaban AMCON, da Buhari ya nada yau

Abubuwa 8 da ya kamata ku sani game da sabon shugaban AMCON, da Buhari ya nada yau

A yau Talata, shugaba Muhammadu Buhar ya nada Mista Edward Adamu a matsayin sabon shugaban hukumar raya dukiyoyi a Najeriya AMCON.

Adamu zai maye gurbin Dakta Muiz Banire, da aka nada a watan Yulin 2018.

Abubuwa 8 da ya kamata ku sani game da sabon shugaban AMCON, da Buhari ya nada yau
Edward adamu
Asali: UGC

Ga abubuwa 8 da ya kamata ku sani akansa:

1. Edward Lametek Adamu kwararran masanin lissafin gine-gine ne kuma dan kasuwa

2. An haifeshi ranar 22 ga Yunin 1959 a Kaltungo jihar Gombe

3. Ya samu digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello dake Zariya

4.Ya tafi karin ilimi a jami'o'i daban-daban a Amurka, Faransa, da Swizalan

5. Yana daya daga cikin mambobin kungiyar kwararrun masu kiyasin gine-gine a Najeriya

6. Adamu ya fara aiki da babbar bankin Najeriya CBN tun shekarar 1992

7. A awatan Febrairun 2018, an nadashi matsayin mataimakin gwamnan babbar bankin Najeiry CBN

8. Edward Adamu nada aure da yara hudu

A wani labarin daban, Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya amince da nada Muhammad M. Nami a matsayin shugaban hukumar kudin shiga ta tarayya, FIRS.

Nami zai maye gurbin Tunde Fowler, wanda wa'adin mulkinsa ya kare a ranar Litinin da ta gabata.

Sabon shugaban hukumar, kwararre ne a bangaren haraji kuma ya kammala karatunsa ne a jami'ar Ahmadu Bello da ke Zaria.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng