An fara tattauna tsakanin Najeriya da Iran kan lamarin El-Zakzaky

An fara tattauna tsakanin Najeriya da Iran kan lamarin El-Zakzaky

Gwamnatocin Najeriya da kasar Iran sun fara tattaunawa na musamman kan shugaban kungiyar mabiyar addinin Shi'an Najeirya, Ibrahim el-Zakzaky.

Ministan harkokin wajen kasar Iran, Seyed Abbas Mousavi, a ranar Lahadi ya bayyana cewa ana yarjejeniya da jami'an Najeriya kan yadda za'a inganta rayuwar El-Zakzaky da ya kasance a tsare tsawon shekaru hudu yanzu.

Ya ce mataimakin shugaban kasan kan tattalin arziki, Mohammed Nahawandian, ya gana da shugaba Muhammadu Buhari a Malabo, kasar Equatorial Guinea, kan lamarin El-Zakzaky.

Ya ce sun gana ne lokacin da suka halarci taron kasashe masu fitar da iskar gas GEC a Equatorial Guinea.

Mousavi yace: "Bangarorin biyu sun tattauna kan hadin kan tattalin arziki, diflomasiyya da kuma lamarin El=Zakzaky."

"Gwamnatin kasar Iran a ganawar da tayi da takwararta Najeriya a Tehran da Abuja, ta tattauna yadda za'a inganta rayuwar Zakzaky a kurkuku."

Babbar kotun tarayya dake zaune a Kaduna ta bada umurnin dauke shugaban kungiyar mabiyar akidar Shi'a a Najeriya, Sheikh Ibrahim Zakzaky, daga ofishin hukumar DSS.

Alkalin ya bayyana cewa a mayar da Sheikh Zazzaky gidan gyara halin jihar Kaduna.

Alkaliy mai shari'a, Jastis Gideon Kudafa, ya bayyana cewa dalilin da yasa a bada wannan umurni shine domin baiwa likitoci da lauyoyin El-Zakzaky daman ganinshi lokacin da suke bukata.

Saboda haka, ya dage karan zuwa ranar 6 ga watan Febrairu, 2019 don cigaba da sauraron.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng