Kyawawan hotunan gada mai hawa 3 da Ganduje ya dandasawa Kanawa
- Gwamnatin jihar Kano, karkashin jagorancin gwamna Dr Abdullahi Umar Ganduje, ta kammala wata katafariyar gadar kasa wacce take da hawa guda uku
- Ana sa ran gadar zata rage mugun cunkoson da ke kan titunan babbar cibiyar kasuwancin ta yankin arewa
- Sai dai kuma, Gwamnan ya yi watsi da harkar ilimi a jihar ta yadda yake tabarbarewa a kullum
Gwamnatin jihar Kano karkashin jagorancon gwamnan jihar Dr Abdullahi Umar Ganduje ta dandasawa mutanen jihar wata gadar kasa mai hawa guda uku.
Gadar na nan a titin Magaji Dambatta, tsohon sha tale-talen Dangi.
Gwamnatin jihar Kano dama ta bayyana cewa, za a kammala gadar cikin rabin shekarar nan ko karshenta.
A kokarin bunkasa aiyuka tare da shawo kan matsalar cunkoson motoci a jihar, gwamnatin na kokari wajen kammala aiyukan tituna gadoji da dai sauransu.
KU KARANTA: Rashin kirkirar sabbin masarautu a Kano shi ya fi alkhairi - Sheikh Daurawa
Sai dai kash! Za a iya cewa gwamnatin jihar Kano din ta yi watsi da harkar ilimi a jihar. A halin yanzu, ilimi ya yi tabarbarewar da za a iya cewa, duk gwamnatocin da suka gabata, babu wacce ta nunawa ilimi halin ko-in-kula kamar wannan gwamnatin.
Sanannen abu ne kuwa, ilimi shine gishirin zaman duniya. Ko a birnin kasuwancin na arewa, ilimi ba karamar rawa zai taka ba wajen bunkasa kasuwancin da wayar da kai.
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu:
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng