Ba zaka taba zama shugaban kasa ba - Anglican Bishop ga El-Rufa'i

Ba zaka taba zama shugaban kasa ba - Anglican Bishop ga El-Rufa'i

Shugaban cocin Anglica na Zariya, Rt Rev Abiodun Ogunyemi, ya ce gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufa'i, ba zai taba zama shugaban kasan Najeriya ba saboda da alamun abinda yake shirin yi kenan a 2023.

Faston ya bayyana hakan ne kan kokarin rusa wani dukiyan Cocin bayan an yi kokarin rusa coci mai tarihin shekaru 110 na George Cathedral, Sabon-Gari Zaria.

Fasto Ogunyemi, ya caccaki takwararsa na garin Wusasa, Rev. Ali Buba Lamido, wanda ya yabawa gwamna El-Rufa'i kan tsagaita rusa cocin ranar Litinin.

Fasto Ogunyemi ya gargadi El-Rufa'i kan kokarin fusata cocin a Kaduna saboda hakan fito-na-fito da Allah ne kuma da Kiristoci a fadin tarayya.

Faston ya ce cocin ba yaki take da gwamnan ba, kawai tana yakin kare hakkinta ne kuma babu wanda zai iya hanasu kwato hakkinsu.

Yace: "Duk wani yunkurin rusa dukiyoyinmu a kasuwa fito-na-fito ne da dukkan Cocina a Najeriya."

"Ana shiryashi domin takara a 2023. Gwamnan ya sani cewa ba zai taba zama shugaban kasa Najeriya ba."

DUBA NAN Yanzu-yanzu: Gwamna Masari ya sake maka Lado da kasa a kotu

Kotun daukaka kara reshen Kaduna a ranar Alhamis, 7 ga watan Nuwamba, ta tabbatar da zaben Malam Nasir Ahmad El-Rufai, a matsayin gwamnan jihar Kaduna a zaben gwamna da aka yi a ranar 9 ga watan Maris, 2019.

Jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) da dan takararta, Isah Ashiru ne suka daukaka kara a gaban kotun, inda suke kalubalantar hukuncin kotun zabe, wacce ta kaddamar da El-Rufai a matsayin wanda ya lashe zaben.

Hukumar zabe mai zaman kanta da fari ta kaddamar da El-Rufai a matsayin wanda ya lashe zaben.

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng