Abubuwa 6 da ya kamata ku sani game Omotunde-Alade, sabuwar hadimar Buhari

Abubuwa 6 da ya kamata ku sani game Omotunde-Alade, sabuwar hadimar Buhari

A yau Talata ne shugaban kasa Muhammadu Buhari ya nada Sarah Omotunde-Alade, a matsayin mai bayar da shawara ta musamman a fannin kudi da tattalin arziki.

Ofishin na nan ne a ma'aikatar kudi, kasafi da tsari na kasa.

Ga wasu abubuwa da yakamata a sani game da Omotunde-Alade:

1. Dakta Sarah Alade ta fara aiki da babban bankin Najeriya ne a shekarar 1993 a matsayin mataimakiyar daraktan bangaren bincike.

2. Ta yi aiki a matsayin shugabar ofishin kudi ta gwamnatin jihohi daga shekarar 1993 zuwa 1996, shugabar ofishin kudi na gwamnatin tarayya daga 1996 zuwa 2000 kuma tayi aiki a sashin kiyasi na haraji daga shekarar 2000 zuwa 2004.

3. An nada Alade a matsayin daraktan aiyukan bankuna ta babban bankin Najeriya a watan Mayu na 2004.

4. Tayi aiki a matsayin shugabar daraktoci, ta tsarin banki da banki kuma tayi sakatariyar kwamitin tsarin biyan kudi na kasa.

5. An zabeta a matsayin mukaddashin gwamnan babban bankin Najeriya a ranar 20 ga watan Fabrairu, 2014 har zuwa lokacin da Godwin Emefiele ya hau kujerar.

6. Dr. Sarah Alade tayi murabus daga babban bankin Najeriya a matsayin mataimakiyar gwamnan bankin bayan shekaru 24 da tayi tana aiki a babban bankin a ranar 22 ga watan Maris, 2017.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164