Tausayi: Bidiyon yadda Sarki Sanusi ya zubar da hawaye yayin bayar da labarin wata mata a Kano

Tausayi: Bidiyon yadda Sarki Sanusi ya zubar da hawaye yayin bayar da labarin wata mata a Kano

Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II a ranar Alhamis ya zubar da hawaye a lokacin da ya ke korafi kan irin talauci da ke adabar al'umma a Najeriya.

A cewarsa, banbanci tsakanin masu kudi da talakawa ya yi yawa sosai kuma talakawan ne ke shan bakar wahala kamar yadda Channels Tv ta ruwaito.

Basaraken ya yi wannan furucin ne a lokacin da ya ke yin jawabi gaban wata kwamiti na Majalisar Dinkin Duniya kan cimma Maradun Karni (SDGs) a jihar Legas.

Ya zubar da hawaye a yayin da ya ke bayar da labarin yadda wani jariri ya mutu a hannun mahaifiyarsa a yayin da ta ke gab da samun taimako.

DUBA WANNAN: Mataimakin gwamna ya kama direbobi da dama masu saba dokokin tuki (Hotuna)

Sanusi ya shaidawa mahalarta taron cewa a ranar, mahaifiyar yaron ta shigo fada daga asibitin yara da ke kilomita 200 daga fadar.

A cewarsa, ya ji ihu mai karfi hakan ya sa ya tura wani ya dubo abinda ke faruwa amma sai mutumin ya dawo cike da hawaye a idonsa.

Sarkin ya ce jaririn ya mutu a hannun mahaifiyarsa yayin da ta ke kan layi tana jira a zo kanta domin ta roki kudin da za ta tafi asibiti a duba mata yaronta.

"Da na tambaya nawa ne kudin, sai aka ce min bai kai dallar Amurka buyar ba," a cewar Sarki Sanusi.

Ya kara da cewa, "irin wannan abubuwan suna faruwa a kullum a kasar. Yara suna mutuwa saboda iyayensu ba su da dallar Amurka biyar, mahaifiya tana kallo yaronta zai mutu saboda ba ta da dalla biyar."

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164