Innalillahi wa’inna illaihi raji’un: An halaka wani jagoran Fulani a Adamawa

Innalillahi wa’inna illaihi raji’un: An halaka wani jagoran Fulani a Adamawa

Yan bindiga sun kashe wani shahararren shugaban Fulani a yankin karamar hukumar Yola ta Kudu da ke jihar Adamawa.

An harbi Alhaji Abdu Bali, Shugaban kungiyar Fulani na Tabbital Pulaku Joondie Jam reshen jihar tare da wani bako a gidansa da misalin karfe 8:00 na daren ranar Talata.

Kakakin rundunar yan sandan jihar, Sulaiman Nguroje, ya tabbatar da harin, cewa rundunar ta fara bincike a lamarin domin gano wadanda suka aikata ta’asar.

Gwamna Ahmadu Fintiri yayi Allah wadai da harin a Wani jawabi daga darakta janar na labaransa a ranar Laraba.

KU KARANTA KUMA: Shugaba Buhari ya nada sabon manajan darakta na NIWA

Jawabin ya kuma yi Allah wadai da kisan Shugaban jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) a unguwar Muchala dale karamar hukumar Mubi ta arewa, Ishaya Dauda, wanda ya afku a ranar Litinin. Ya Kara da cewa gwamnan ya bukaci yan sanda da su tsamo makasan shugabannin biyu domin fuskantar shari’a.

A halin da ake ciki, Legit.ng ta rahoto a baya cewa 'Yan bindiga sun kashe dan majalisa, Venture Kagbude a karamar hukumar Sapele ta jihar Delta.

Jaridar Punch ta ruwaito cewa, ana zargin hayar 'yan bindigar hayarsu aka yi don kashe dan majalisar inda kuwa suka kashesa a ranar Talata, 1 ga watan Oktoba, 2019 akan titin Warri.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng