Kyan alkawari cikawa: Gwamna El-Rufa'i ya kai yaronsa makarantar gwamnati (Hotuna)

Kyan alkawari cikawa: Gwamna El-Rufa'i ya kai yaronsa makarantar gwamnati (Hotuna)

Kamar yadda yayi alkawari a shekaru biyu da suka gabata, gwamnan jihar Kaduna, Nasir Ahmed El-Rufa'i, ya shigar da yaronsa, Abubakar Al-Siddique El Rufa'i, makarantar gwamnatin Kaduna Capital School dake unguwar Malali Kaduna.

Gwamnan tare da amaryarsa sun kai Abubakar mai shekaru 6 da haihuwa makarantar inda zai yi karatun firamarensa.

Wanna labari ya bayyana ne da safiyar Litinin a shafin ra'ayi da sada zumuntar fadar gwamnan jihar inda tace:

"A ranar 28 ga Disamban 2017, Malam Nasir El-Rufa'i yace ' Ni da kaina zan tabbatar da cewa yarona da zai isa shekaru shida a 2019, zan kaishi makarantar gwamnati a jihar Kaduna, idan Allah ya yarda."

"Kawo sauyi bangaren ilimin jihar Kaduna ijtihadi ne zamu cigaba da yi bayan shekarun da aka gurbatashi. Gwamnatin El-Rufai ta lashi takobin gyara makarantun gwamnati da kuma farfado da mutuncinsu ta yadda masu kudi kadai zasu rika kai yaransu makarantan kudi."

Kalli hotunan:

Kyan alkawari cikawa: Gwamna El-Rufa'i ya kai yaronsa makarantar gwamnati (Hotuna)
Kyan alkawari cikawa
Asali: Facebook

KU KARANTA: Rufe iyakokin Najeriya ya hana fasa kwabrin man fetur kimanin lita milyan 11

Kyan alkawari cikawa: Gwamna El-Rufa'i ya kai yaronsa makarantar gwamnati (Hotuna)
Gwamna El-Rufa'i ya kai yaronsa makarantar gwamnati (Hotuna)
Asali: Facebook

Kyan alkawari cikawa: Gwamna El-Rufa'i ya kai yaronsa makarantar gwamnati (Hotuna)
Kyan alkawari cikawa: Gwamna El-Rufa'i ya kai yaronsa makarantar gwamnati (Hotuna)
Asali: Facebook

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel