Kyan alkawari cikawa: Gwamna El-Rufa'i ya kai yaronsa makarantar gwamnati (Hotuna)

Kyan alkawari cikawa: Gwamna El-Rufa'i ya kai yaronsa makarantar gwamnati (Hotuna)

Kamar yadda yayi alkawari a shekaru biyu da suka gabata, gwamnan jihar Kaduna, Nasir Ahmed El-Rufa'i, ya shigar da yaronsa, Abubakar Al-Siddique El Rufa'i, makarantar gwamnatin Kaduna Capital School dake unguwar Malali Kaduna.

Gwamnan tare da amaryarsa sun kai Abubakar mai shekaru 6 da haihuwa makarantar inda zai yi karatun firamarensa.

Wanna labari ya bayyana ne da safiyar Litinin a shafin ra'ayi da sada zumuntar fadar gwamnan jihar inda tace:

"A ranar 28 ga Disamban 2017, Malam Nasir El-Rufa'i yace ' Ni da kaina zan tabbatar da cewa yarona da zai isa shekaru shida a 2019, zan kaishi makarantar gwamnati a jihar Kaduna, idan Allah ya yarda."

"Kawo sauyi bangaren ilimin jihar Kaduna ijtihadi ne zamu cigaba da yi bayan shekarun da aka gurbatashi. Gwamnatin El-Rufai ta lashi takobin gyara makarantun gwamnati da kuma farfado da mutuncinsu ta yadda masu kudi kadai zasu rika kai yaransu makarantan kudi."

Kalli hotunan:

Kyan alkawari cikawa: Gwamna El-Rufa'i ya kai yaronsa makarantar gwamnati (Hotuna)
Kyan alkawari cikawa
Asali: Facebook

KU KARANTA: Rufe iyakokin Najeriya ya hana fasa kwabrin man fetur kimanin lita milyan 11

Kyan alkawari cikawa: Gwamna El-Rufa'i ya kai yaronsa makarantar gwamnati (Hotuna)
Gwamna El-Rufa'i ya kai yaronsa makarantar gwamnati (Hotuna)
Asali: Facebook

Kyan alkawari cikawa: Gwamna El-Rufa'i ya kai yaronsa makarantar gwamnati (Hotuna)
Kyan alkawari cikawa: Gwamna El-Rufa'i ya kai yaronsa makarantar gwamnati (Hotuna)
Asali: Facebook

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng