Kalli ma’aikatun da gwamnan Bauchi ya tura sabbin kwamishinonin jahar guda 20

Kalli ma’aikatun da gwamnan Bauchi ya tura sabbin kwamishinonin jahar guda 20

Wata sanarwa daga fadar gwamnatin jahar Bauchi dake dauke da sa hannun sakataren gwamnatin jahar Bauchi, Mohammed Sabiu Baba ta bayyana ma’aikatun da gwamnan jahar Bauchi, Sanata Bala Muhammad ya tura sabbin kwamishinoninsa.

Rahoton jaridar Daily Trust ta bayyana sanarwar ta ce: “Biyo bayan rantsar da sabbin mambobin majalisar zartarwar jahar Bauchi a ranar 6 ga watan Satumba, mai girma gwamnan jahar Bauchi, Sanata Bala Abdulkadir Muhammd ya amince da turasu ma’aikatun da za su yi aiki.”

KU KARANTA: Shugaban kungiyar Malamai ASUU ya yi ma Sanatoci albishir

Majiyar Legit.ng ta ruwaito ma’aikatun da gwamnna ya tura sabbin kwamishinonin sune kamar haka;

Alhaji Nura Manu Soro, ma’aikatan kudi

Dakta Ladan Salihu, ma’aikatan watsa labaru da sadarwa

Dakta Aliyu Usman Tilde, ma’aikatan ilimi

Farfesa Adamu Ahmed, ma’aikatan filaye da sifiyo

Abdulkadir Ibrahim, ma’aikatan ayyuka da sufuri

Jidauna Tula Mbami, ma’aikatan kungiyoyi da cigaban kasuwanci

Dakta Aminu Hassan Gamawa ma’aikatan kasafin kudi da tsare tsare

Hajara Jibrin Gidado, ma’aikatan kula da mata da hakkokin yara

Turaki Mohammed Manga, kwamishinan ayyuka na musamman

Abdulrazak Nuhu Zaki, ma’aikatan kananan hukumomi da masarautun gargajiya

Ahmed Aliyu Jalam, ma’aikatan addini

Modibbo U.A Ahmed, ma’aikatan al’adun gargajiya da bude ido

Sama’ila Ibn Adamu, ma’aikatan noma da cigaban karkara

Barrister Yakubu Bello Kirdi, ma’aikatan sharia

Hamish M. Shira, ma’aikatan muhalli da gidaje

Mohammed A. Sadiq, ma’aikatan ciniki da masana’antu

Umaru Sanda Adamu, ma’aikatan ruwa

Auwal Mohammed Jatau, ma’aikatan kiwon lafiya

A wani labarin kuma, Kotun sauraron korafe korafen zaben gwamnan jahar Kaduna da aka gudanar a watan Maris na shekarar 2019 ta tabbatar da nasarar da Nasir Ahmad El-Rufai ya samu, inda ta bayyana shi a matsayin halastaccen gwamnan jahar.

Ku biyo mu a https://facebook.com/legitnghausa

ko a http://twitter.com/legitcomhausa

KU LATSA: Hanyar sauko da sabuwar manhajar jaridar Legit.com Hausa cikin sauki

Ga masu shawara ko korafi, a same mu a labaranhausa@corp.legit.com

Sanarwa na musamman: Shafin NAIJ Hausa ya koma Legit Hausa

Asali: Legit.ng

Tags:
Online view pixel