Makarantar horar da ‘yan sanda ta Wudil ta sanya ranar jarabawar sabbin shiga

Makarantar horar da ‘yan sanda ta Wudil ta sanya ranar jarabawar sabbin shiga

-Makarantar horar da 'yan sanda ta Wudil za ta gudanar da jarabawar sabbin shiga ranar Asabar 24 ga Agusta

-Kakakin rundunar 'yan sandan Legas DSP Bala Elkana ne ya fitar da wannan sanarwa ranar Alhamis 22 ga watan Agusta

-Za a fara wannan jarabawar ne da misalin karfe 7 na safiyar Asabar kamar yadda ya fadi cikin sanarwar tasa

Rundunar ‘yan sandan jihar Legas ta sanar da daliban da suka nemi samun gurbin karatu a makarantar horar da ‘yan sanda ta Wudil wato Nigerian Police Academy, Kano cewa za a rubuta jarabawar sabbin shiga a ranar Asabar 24 ga watan Agusta.

Majiyar da ta kawo mana wannan labarin ta ce kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Legas DSP Bala Elkana ne ya bada wannan sanarwar a ranar Alhamis 22 ga watan Agusta inda yake cewa cibiyoyi rubuta jarabawar a Legas sun hada da, Kwalejin ‘yan sanda ta Ikeja, Kings College da Makarantar mata ta Anwarul Islam.

KU KARANTA:Mamakon ruwan sama ya yi awon gaba da kananan yara 3 a jahar Kano

A zancen da rundunar da fitar ta sanar da masu rubuta jarabawar cewa kowa ya fidda katinsa na jarabawar a yanar gizo kuma dole ne mutum ya kasance a wurin rubuta jarabawar da karfe 7 daidai na ranar jarabawar.

Ga abinda zance yake fadi: “ Rundunar ‘yan sandan Jihar Legas na farin cikin sanar da al’umma cewa Makarantar horar da ‘yan sanda ta Wudil za ta rubuta jarabawar sabbin shiga rukuni na 7 a ranar Asabar 24 ga watan Agusta.

“ Wuraren rubuta jarabawar su ne kamar haka, Kwalejin ‘yan sanda ta Ikeja, Kings College Obalende da kuma Makarantar mata ta Anwarul Islam.

“ Ana shawartar ko wane dalibin da zai rubuta wannan jarabawar da ya fitar da katinsa na rubuta jarabawa daga shafin yanar gizo. Sannan kuma kowa ya kasance a wurin rubuta jarabawar kafin karfe 7 na safiyar ranar Asabar.”

Ku biyo mu a https://facebook.com/legitnghausa

ko a http://twitter.com/legitcomhausa

KU LATSA: Hanyar sauko da sabuwar manhajar jaridar Legit.com Hausa cikin sauki

Ga masu shawara ko korafi, a same mu a labaranhausa@corp.legit.com

Sanarwa na musamman: Shafin NAIJ Hausa ya koma Legit Hausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng

Online view pixel