An hana wata mata zaman majalisa yayin da ta shigo da jaririya rike a hannunta (Hotuna)

An hana wata mata zaman majalisa yayin da ta shigo da jaririya rike a hannunta (Hotuna)

Majalisar dokokin Kenya ta umarci Zulekha Hassan ta fita daga cikin majalisar a dalilin shigowa da tayi rike da jaririyarta ranar Laraba.

An hana wata mata zaman majalisa yayin da ta shigo da jaririya rike a hannunta (Hotuna)
Zulekha Hassan
Asali: Twitter

KU KARANTA:Ni ne nan jagoran ‘inconclusive’ – Ganduje

Zulekha Hassan na daya daga cikin mambobin majalisar dokokin Kenya. Kakakin majalisar, Hon. Chris Omulele ya bayyana wannan abinda Zulekha tayi a matsayin sabawa doka.

An hana wata mata zaman majalisa yayin da ta shigo da jaririya rike a hannunta (Hotuna)
Majalisar dokokin Kenya
Asali: Twitter

Matar wadda take wakiltar matan Kwale a majalisar ta ce, akwai uzurin da take da shi na gaggawa wanda ya sanyata zuwa da jariryar har cikin majalisa.

An hana wata mata zaman majalisa yayin da ta shigo da jaririya rike a hannunta (Hotuna)
Majalisar dokokin Kenya
Asali: Twitter

“ Nayi kokarin zuwa ba tare da diyata ba, amma hakan bai yiwu ba saboda uzurin da nake da shi. Me ya kamata nayi a cikin wannan halin? Da ace akwai dakin renon yara a nan cikin majalisa ai da na kai diyata can.” A cewar Zulekha.

Ku biyo mu a https://facebook.com/legitnghausa

ko a http://twitter.com/legitcomhausa

KU LATSA: Hanyar sauko da sabuwar manhajar jaridar Legit.com Hausa cikin sauki

Ga masu shawara ko korafi, a same mu a labaranhausa@corp.legit.com

Sanarwa na musamman: Shafin NAIJ Hausa ya koma Legit Hausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel