An damke matashin da ya hallaka mahaifinsa a Jigawa

An damke matashin da ya hallaka mahaifinsa a Jigawa

Jami'an yan sandan jihar Jigawa sun damke wani matashi dan shekara 25, Jamilu Harisu, da laifin kashe mahaifinsa mai shekaru 70.

Matashin, wanda ake zargi ya aikata aika-aikan ne saboda ya debi kwayoyi kafin ya kai wa mahaifinsa hari a gona.

Harisu ya kashe mahaifinsa ne a kauyen Makku dake karamar hukumar Garki na jihar Jigawa, inda ya buga masa fatanya a kai.

Kakakin hukumar yan sandan jihar, SP Audu Jinjiri, ya tabbatar da cewa mahaifin ya kwanta dama a asibitin Garki.

Yace: "Tuni yan sanda sun damkeshi da laifin kisan kai. An aika takardar tuhumarsa sashen binciken hukumar domin gudanar da bincike kafin gurfanar da shi."

A bangare guda, Kwana biyu kenan ana zub da jini a birnin tarayya Abuja yayinda yan kungiyar IMN wadanda akafi sani da yan Shi'a suka sake gwabzawa da jami'an yan sandan Najeriya a zanga-zangar da suka gudanar a shahrarriyar kasuwar Banex dake Wuse Abuja.

Bisa ga rahoton da yan sandan suka samu cewa yan Shi'an zasu fito yau misalin karfe 2 na rana, sai suka tare hanyar domin hanasu.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng