Yanzu-yanzu: Yan Shi'a sun bankawa ma'aikatar NEMA wuta

Yanzu-yanzu: Yan Shi'a sun bankawa ma'aikatar NEMA wuta

A yanzu haka, wani sashen ma'aikatar hukumar bada agaji na gaggawa ta kasa wato NEMA dake Abuja na ci bal-bal.

Hakazalika an bankawa motocin hukumar biyu wuta kuma jami'an kwana-kwana na cikin kashe wutan yanzu.

A cewar The Cable, Wani mai idon shaida ya bayyanawa manema labarai cewa yan kungiyar Shi'a mabiya Sheik Ibrahim El-Zakzaky da suke gudanar da zanga-zanga suka bankawa ma'aikatar wuta lokacin da yan sanda suka hanasu zanga-zanga.

Zanga-zangar wacce suka fara daga tashan NITEL Junction dake Wuse 2 ya samu cikas ne yayinda yan sanda suka toshe hanyar zuwa majalisar dokokin tarayya da fadar shugaba kasa

Kawai sai yan sanda suka fara harbe-harbe yayinda yan Shi'an ke kokarin shiga farfajiyar Eagle Square. Akalla mutane biyu sun rasa rayukansu kawo yanzu.

Wani dan Shi'a yace: "Za mu cigaba da zanga-zanga, kuma idan basu son ganinmu a kan titi, gwamnati ta saki shugabanmu. Idan suna son kashe, su cigaba da kashemu."

Yanzu-yanzu: Yan Shi'a sun bankawa ma'aikatar NEMA wuta
Gawar wani da aka kashe
Asali: Facebook

Bidiyo:

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng