Yanzu-yanzu: Yan Shi'a sun bankawa ma'aikatar NEMA wuta
A yanzu haka, wani sashen ma'aikatar hukumar bada agaji na gaggawa ta kasa wato NEMA dake Abuja na ci bal-bal.
Hakazalika an bankawa motocin hukumar biyu wuta kuma jami'an kwana-kwana na cikin kashe wutan yanzu.
A cewar The Cable, Wani mai idon shaida ya bayyanawa manema labarai cewa yan kungiyar Shi'a mabiya Sheik Ibrahim El-Zakzaky da suke gudanar da zanga-zanga suka bankawa ma'aikatar wuta lokacin da yan sanda suka hanasu zanga-zanga.
Zanga-zangar wacce suka fara daga tashan NITEL Junction dake Wuse 2 ya samu cikas ne yayinda yan sanda suka toshe hanyar zuwa majalisar dokokin tarayya da fadar shugaba kasa
Kawai sai yan sanda suka fara harbe-harbe yayinda yan Shi'an ke kokarin shiga farfajiyar Eagle Square. Akalla mutane biyu sun rasa rayukansu kawo yanzu.
Wani dan Shi'a yace: "Za mu cigaba da zanga-zanga, kuma idan basu son ganinmu a kan titi, gwamnati ta saki shugabanmu. Idan suna son kashe, su cigaba da kashemu."
Bidiyo:
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng