An damke yan luwadi biyu a birnin tarayya, Abuja

An damke yan luwadi biyu a birnin tarayya, Abuja

Hukumar yan sanda a ranar Alhamis ta gurfanar da wasu matasa biyu a kotun Grade 1 dake unguwar Kabusa Abuja kan tuhumar aikata luwadi.

Matasan biyu masu suna, John Samuel da Mohammed Sani mazauna unguwar Dakwa ne a cikin birnin tarayya Abuja.

Lauyan gwamnati, John Ijagbemi, ya bayyanawa kotu cewa wadannan matasa sun aikata aikin alfashan ne ranar 18 ga watan Yuni, 2019.

John Ijagbemi ya bayyana cewa a ranar 18 ga Yuni misalin karfe 1:30 na dare, jami'an yan sandan Garki, birnin tarayya masu sintiri sun damke matasan suna luwadi da juna a unguwar Garki.

Ya laburtawa kotu cewa yayin bincike, an gano cewa matasan sun kasance suna aikata luwadi tun shekarar 2018.

KU KARANTA: Bayan makonni takwas, gwamnoni 26 basu nada kwamishanoni na

Alkalin kotun, Aliyu Kagarko, ya basu beli milyan biyu-biyu da wanda zai tsaya musu. An dakatad da karan zuwa ranar 25 ga Yuli, 2019.

Mun kawo muku rahoton cewa Fitacciyar mawakiyar 'Pop' din nan Janet Jackson kanwa a gurin shaharren marigayin mawakin nan Micheal Jackson, ta na daya daga cikin shahararrun mawakan da zasu yi waka a kasar Saudiyya.

Bayan ita kuma akwai shahararren mawakin nan na 'Rap' 50 Cent wanda shima zai je kasar ya baza tashi iyawar. Rahotanni sun nuna a satin da Nicki Minaj ta nuna cewar baza tayi wasan a kasar ba, sai aka gayyato wadannan mawakan guda biyu.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng