Yar’ uwar Shugaba Buhari mai shekaru 84 ta yi tafiyar mita 100 don yin zabe

Yar’ uwar Shugaba Buhari mai shekaru 84 ta yi tafiyar mita 100 don yin zabe

- Babbar yayar Shugaban kasar Muhammadu Buhari, Hajiya Rakiya Adamu-Amadodo ta gudanar da aikin da ya rataya a wuyanta a matsayinta na yar kasa mai yanci

- Rakiya mai shekaru 84 yi tattaki har tsawon mita 100 da kafa domin yin zaben gwamna da na majalisar jiha

- Ta samu rakiyar jikarta da kuma wasu abokan arziki

Hajiya Rakiya Adamu-Amadodo, babbar yayar Shugaban kasar Muhammadu Buhari da ta rage a ranar Asabar, 9 ga watan Maris ta gudanar da aikin da ya rataya a wuyanta a matsayinta na yar kasa mai yanci inda ta kada kuri’ arta na zaben gwamna da majalisar dokoki.

Kamfanin dillancin labaran Najeriya (NAN) a Daura ta ruwaito cewa yar’ uwar Shugaban kasar ta yi tafiyar mita 100 a kafa zuwa mazabar Kofar Baru 002 da ke Daura domin yin zabenta da misalin karfe 12:34 na rana.

Yar’ uwar Shugaba Buhari mai shekaru 84 ta yi tafiyar mita 100 don yin zabe
Yar’ uwar Shugaba Buhari mai shekaru 84 ta yi tafiyar mita 100 don yin zabe
Asali: UGC

Legit.ng ta tattaro cewa Adamu-Amadodo ta samu rakiyar jikanta, yan’ uwa da abokan arziki zuwa wajen zaben.

Akalla mutane 854 aka yiwa rijista a mazabarta.

KU KARANTA KUMA: Kai-tsaye: Yadda zaben gwamnoni da 'yan majalisun jihohi ke gudana a Nasarawa, Niger da Kwara

Da farko Legit.ng ta rahoto cewa Shugaba Muhammadu Buhari da safiyar Asabar ya kada kuri'arsa a Kofar Baru, PU 003 dake garin Daura, jihar Katsina. Ya kada kuri'arsa ne tare da uwargidarsa, Hajiya Aisha Buhari misalin karfe 8;04 na safe.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: : https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng