Magoya bayan PDP 2,509 sun sauya sheka zuwa APC a Katsina
- Mambobin jam’iyyar PDP 2,509 sun sauya sheka zuwa jam’iyyar APC a jihar Katsina
- Gwamna Aminu Masari ne ya tarbi masu sauya shekar a Sandamu lokacin kamfen dinsa a yankin
- Masari ya bayyana tarin ayyukan ci gaba da gwamnatinsa ta kaddamar a fadin jihar
Rahotanni sun kawo cewa akala mambobin jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP), 2,509 suka sauya sheka a ranar Litinin, 28 ga watan Janairu zuwa jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a karamar hukumar Sandamu da ke jihar Katsina.
Gwamna Aminu Masari ne ya tarbi masu sauya shekar a Sandamu lokacin kamfen dinsa a yankin.
Yace gwamnatinsa za ta fara aikin gyaran babban asibitin Sandamu da gyara hanyoyin garin a fadin sassa goma sha daya na yankin nan ba da jimawa ba.

Asali: UGC
Masari ya bayyana cewa gwanatinsa ta yi ayyukan ci gaba da dama ciki harda hanyar kilomita 40 na Fago- Katsayal- Kwasarawa-Jirdede-Koza.
KU KARANTA KUMA: Zabe: Ku zabi shugaba mai gaskiya da rikon amana - Sheikh Bala Lau
Ya kuma bayyana cewa hanyoyin sun hade aruruwa a yankin da kuma na karamar hukumar Maiadua.
Gwamnan ya ara da cewa gwamnatinsa ta kuma sabonda hanyar Sandamu-Baure- Babban Mutum na tsawon kilomita 75 da kuma rijiyyin ruwa 150.
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayarku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukan mu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Shafin Naij.com Hausa ya koma Legit.ng Hausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng