Magoya bayan PDP 2,509 sun sauya sheka zuwa APC a Katsina
- Mambobin jam’iyyar PDP 2,509 sun sauya sheka zuwa jam’iyyar APC a jihar Katsina
- Gwamna Aminu Masari ne ya tarbi masu sauya shekar a Sandamu lokacin kamfen dinsa a yankin
- Masari ya bayyana tarin ayyukan ci gaba da gwamnatinsa ta kaddamar a fadin jihar
Rahotanni sun kawo cewa akala mambobin jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP), 2,509 suka sauya sheka a ranar Litinin, 28 ga watan Janairu zuwa jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a karamar hukumar Sandamu da ke jihar Katsina.
Gwamna Aminu Masari ne ya tarbi masu sauya shekar a Sandamu lokacin kamfen dinsa a yankin.
Yace gwamnatinsa za ta fara aikin gyaran babban asibitin Sandamu da gyara hanyoyin garin a fadin sassa goma sha daya na yankin nan ba da jimawa ba.
Masari ya bayyana cewa gwanatinsa ta yi ayyukan ci gaba da dama ciki harda hanyar kilomita 40 na Fago- Katsayal- Kwasarawa-Jirdede-Koza.
KU KARANTA KUMA: Zabe: Ku zabi shugaba mai gaskiya da rikon amana - Sheikh Bala Lau
Ya kuma bayyana cewa hanyoyin sun hade aruruwa a yankin da kuma na karamar hukumar Maiadua.
Gwamnan ya ara da cewa gwamnatinsa ta kuma sabonda hanyar Sandamu-Baure- Babban Mutum na tsawon kilomita 75 da kuma rijiyyin ruwa 150.
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayarku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukan mu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Shafin Naij.com Hausa ya koma Legit.ng Hausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng