Magoya bayan PDP 2,509 sun sauya sheka zuwa APC a Katsina

Magoya bayan PDP 2,509 sun sauya sheka zuwa APC a Katsina

- Mambobin jam’iyyar PDP 2,509 sun sauya sheka zuwa jam’iyyar APC a jihar Katsina

- Gwamna Aminu Masari ne ya tarbi masu sauya shekar a Sandamu lokacin kamfen dinsa a yankin

- Masari ya bayyana tarin ayyukan ci gaba da gwamnatinsa ta kaddamar a fadin jihar

Rahotanni sun kawo cewa akala mambobin jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP), 2,509 suka sauya sheka a ranar Litinin, 28 ga watan Janairu zuwa jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a karamar hukumar Sandamu da ke jihar Katsina.

Gwamna Aminu Masari ne ya tarbi masu sauya shekar a Sandamu lokacin kamfen dinsa a yankin.

Yace gwamnatinsa za ta fara aikin gyaran babban asibitin Sandamu da gyara hanyoyin garin a fadin sassa goma sha daya na yankin nan ba da jimawa ba.

Magoya bayan PDP 2,509 sun sauya sheka zuwa APC a Katsina
Magoya bayan PDP 2,509 sun sauya sheka zuwa APC a Katsina
Asali: UGC

Masari ya bayyana cewa gwanatinsa ta yi ayyukan ci gaba da dama ciki harda hanyar kilomita 40 na Fago- Katsayal- Kwasarawa-Jirdede-Koza.

KU KARANTA KUMA: Zabe: Ku zabi shugaba mai gaskiya da rikon amana - Sheikh Bala Lau

Ya kuma bayyana cewa hanyoyin sun hade aruruwa a yankin da kuma na karamar hukumar Maiadua.

Gwamnan ya ara da cewa gwamnatinsa ta kuma sabonda hanyar Sandamu-Baure- Babban Mutum na tsawon kilomita 75 da kuma rijiyyin ruwa 150.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayarku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukan mu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Shafin Naij.com Hausa ya koma Legit.ng Hausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng