Buhari shugaba ne mai amana – Shugaban kungiyar Qadiriyya

Buhari shugaba ne mai amana – Shugaban kungiyar Qadiriyya

- Shugaban kungiyar Qadiriyya a Afrika, Sheikh Qaribullah Nasir-Kabara ya bayyana Buhari a matsayin shugaba mai amana

- Sheikh Kabara ya bayyana hakan ne a lokacin bikin maulidin da aka gudanar a Kano

- Ya nuna goyon baya ga shugaban kasa a kokarinsa na daidaita amuran Najeriya akan tafarkin ci gaba

Shugaban kungiyar Qadiriyya a Afrika, Sheikh Qaribullah Nasir-Kabara ya bayyana shugaban kasa Muhammadu Buhari a matsayin shugaba mai amana da sauraron matsalolin jama’a.

Shugaban kungiyar ya bayyana hakan ne a lokacin bikin maulidin da aka gudanar a Kano.

Nasiru-Kabara yace shugaba Buhari na da son ci gaban kasar a zuciyarsa sannan kuma ya kamata duk masu son ci gaban Najeriya su mara masa baya.

Buhari shugaba ne mai amana – Shugaban kungiyar Qadiriyya
Buhari shugaba ne mai amana – Shugaban kungiyar Qadiriyya
Asali: Twitter

Ya tuna cewa a lokacin ziyarar da shugabannin suka kaiwa shugaban kasar a fadarsa a kwanakin baya yace anyi gaggawar magance wasu matsaloli da suka gabatarwa gwamnati.

KU ARANTA KUMA: Bana tsoron Buhari, Allah kadai nake tsoro – Gwamna Amosun

Ya nuna goyon baya ga shugaban kasa a kokarinsa na daidaita amuran Najeriya akan tafarkin ci gaba.

Kamfanin dillancin labaran Najeriya ta ruwaito cewa shugaban kasar wanda ya samu wakilin babban sakataren kungiyar TETfund, Dr Abdullahi Baffa-Bichi, ya sake tabbatar da jajircewarsa wajen ci gaban kasar.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: : https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng