2019: Jami'ar Cambridge ta kasar Ingila ta gayyaci 'yan takarar shugaban kasa 5

2019: Jami'ar Cambridge ta kasar Ingila ta gayyaci 'yan takarar shugaban kasa 5

Hukumar jami'ar Cambridge da hadin gwuiwar kungiyar daliban nahiyar Afrika dake karatu a makarantar (CUACS) sun kammala shirin gayyatar 'yan takarar kujerar shugaban kasa 5 daga Najeriya domin tattaunawa ta musamman dangane da zaben shekarar 2019.

Taron mai taken '2019 Nigerian Presidential Forum', za a gudanar da shi a watan Janairu na shekarar 2019.

A wata sanarwa da masu shirya taron suka fitar a jiya, Laraba, sun bayyana cewar tattaunawar zata bawa 'yan takarar damar ganawa da 'yan Najeriya dake kasar Ingila.

2019: Jami'ar Cambridge ta kasar Ingila ta gayyaci 'yan takarar shugaban kasa 5
2019: Jami'ar Cambridge ta kasar Ingila ta gayyaci 'yan takarar shugaban kasa 5
Asali: Twitter

DUBA WANNAN: Atiku ya fadawa CAN nufinsa ga Najeriya

Martine Dennis, dan jaridar kasar Ingila, ne zai zama mai gabatawa yayin tattaunawar.

"A yayin da Najeriya ke shirin yin zaben shugaban kasa a ranar 16 ga watan Fabrairu na shekarar 2019, wannan tattaunawar zata bawa 'yan takara damar bayyana manufofinsu ga Najeriya," a cewar sanarwar.

"Mun shirya gayyatar 'yan takara biyar; shugaba Muhammadu Buhari, Atiku Abubakar, Oby Ezekwesili, Kingsley Chiedu Moghalu, da Donald Duke, bisa la'akari da mukaman da suka rike a baya."

Wata kididdigar alkaluman daliban kasashen ketare dake karatu a kasar Ingila ta nuna cewar akwai a kalla 'yan Najeriya 20,000 dake karatu a jami'o'i daban-daban dake kasar Ingila.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: : https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng