Yawan kudin da yan Najeriya ke kashewa wajen tafiya karatu a kasashen waje duk shekara
Shugaban Jami’ar Crawford, kuma tsohon Shugaban Jami’ar Lagas, Farfesa Oye Ibidapo-Obe, ya bayyana cewa ‘yan Najeriya na kashe kimanin naira tiriliyan daya a duk shekara wajen tafiya kasashen waje domin yin karatun digiri.
Farfesa Oye Ibidapo-Obe, ya bayyana cewa ‘yan Najeriya na kashe kimanin naira tiriliyan daya a duk shekara wajen tafiya kasashen waje domin yin karatun digiri
Ya bayyana hakan ne a ranar Laraba, 12 ga watan Disamba yayinda ya ke jawabi a bikin yaye dalibai karo na 10 na Jami’ar Crawford da ke garin Igbesa, jihar Ogun.

Asali: UGC
Ya tona yadda ake kashe wadannan makudan kudade ne, daidai lokacin da malaman jami’o’in Najeriya ke ci gaba da gudanar da yajin aikin da suka fara tun daga ranar 4 ga watan Nuwamba.
Daga nan ya ci gaba da nuna muhimmancin ci gaba da kafa jami’o’i masu zaman kan su wadanda ba na gwamnati ba.
KU KARANTA KUMA: Shugabancin kasa: Abokin takarar Donald Duke ya janye daga tseren
Ya ce ta haka ne za su kara samun ingancin da za a rage karakainar neman karin ilmi a kasashen duniya, inda ake kwasar makudan kudade ana tafiya da sunan tafiya karin ilmi.
Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Ku same mu a https://www.facebook.com/legitnghausa
Ko a http://twitter.com/legitnghausa
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta LEGIT NG Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Shafin NAIJ Hausa ya koma LEGIT
Asali: Legit.ng