Idan Inyamurai su na son mulkin Najeriya cikin ruwan sanyi, su zabi Buhari – Ngige

Idan Inyamurai su na son mulkin Najeriya cikin ruwan sanyi, su zabi Buhari – Ngige

- Dr. Chris Ngige yayi kira ga mutanen Kudu su marawa Shugaba Buhari baya a 2019

- Ngige yayi kira ga Inyamurai su yi watsi da tayin Mataimakin Shugaban kasa a PDP

- Ministan yace idan Buhari ya kammala wa’adin sa, Ibo za su karbi mulkin kasar nan

Idan Inyamurai su na son mulkin Najeriya cikin ruwan sanyi su zabi Buhari – Ngige
Ngige yace saura shekaru 4 Ibo su karbi mulkin Najeriya a APC
Asali: Depositphotos

Ministan kwadago na Kasar nan, Chris Ngige, yayi kira ga Mutanen Kudu maso Gabashin Kasar nan da su fito su marawa Shugaban kasa Muhammadu Buhari baya a zaben badi na 2019 domin su samu mulkin kasar nan a 2023.

Kamar yadda mu ka samu labari, Chris Ngige yayi wannan jawabi ne jiya Lahadi a Karamar Hukumar Idemili ta Arewa da ke cikin Jihar Anmabra. Ministan yace idan har Buhari ya kammala wa’adin sa, Inyamurai za su gaje sa.

KU KARANTA: Afuwa ya kamata PDP ta nema a Najeriya ba nemen mulki ba - APC

Jaridar Punch ta rahoto Ministan yana jan hankalin Inyamurai su yi watsi da kujerar Mataimakin Shugaban kasa da aka ba su a PDP, su marawa Buhari baya ya koma kan karaga, domin ya karasa shekaru 4 da su ka rage masa.

Ngige yace idan Inyamurai su kayi sake, Yarbawa za su karbe mulkin Kasar bayan Shugaba Buhari. Babban Ministan yace tuni tsohon Gwamnan Legas kuma Minista a yanzu Babatude Fashola ya fasa kwan irin shirin da Yarbawa ke yi.

Dr. Ngige ya bayyana cewa tayin Mataimakin Shugaban kasa da Atiku Abubakar yayi wa Mutanen sa a PDP ba komai bane domin kuwa mukamin bai wuce na je-ka-na-yi-ka ba, don haka ya roki Inyamurai su kama jirgin APC domin su tsira.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/legitnghausa

Ko a http://twitter.com/legitnghausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta LEGIT NG Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Shafin NAIJ Hausa ya koma LEGIT

Asali: Legit.ng

Online view pixel