Sarki ya nada wa mata 5 sarauta a Gombe

Sarki ya nada wa mata 5 sarauta a Gombe

- Sarkin Deba da ke jihar Gombe, Alhaji Ahmed Usman ya nada wa mata biyar sarauta

- An gudanar da bikin nadin sarautar ne a fadar sarkin da ke karamar hukumar Yamaltu/Deba na jihar a yau Juma’a

- Usman ya bayyana cewa mata na iya bakin kokarinsu a masarautar inda ya kara da cewa suna da muhimmin rawar ganin takawa a masarautar

Sarkin Deba da ke jihar Gombe, Alhaji Ahmed Usman ya nada wa mata biyar sarauta a masarautar shi.

An gudanar da bikin nadin sarautar ne a fadar sarkin da ke karamar hukumar Yamaltu/Deba na jihar a ranar Juma’a, 7 ga watan Disamba.

Sarki ya nada wa mata 5 sarauta a Gombe
Sarki ya nada wa mata 5 sarauta a Gombe
Asali: Twitter

Kamfanin dillancin labarai na Najeriya (NAN) ta ruwaito cewa wadanda aka nada wa sarautar sun hada da Fatima Mohammed a matsayin Garkuwan Matan Deba na farko da Aisha Muhammed a matsayin Annurin Deba.

Sauran sune Halima Muhammed a matsayin Tauraruwan Deba, Kulu Tela-Sidi a matsayin Walkiyan Matan Deba sannan Abu Gurkuma a matsayin Sarkin Kudun Deba.

Da yake Magana a wajen taron, sarkin ya bayyana cewa matan sun samu tarin nasarori a bangaren ayyukansu.

KU KARANTA KUMA: Dokar zabe: Ku bi ta kan Shugaba Buhari – PDP ga majalisar dokokin kasar

Usman ya bayyana cewa mata na iya bakin kokarinsu a masarautar inda ya kara da cewa suna da muhimmin rawar ganin takawa a masarautar.

Ya yi kira a gare su da su riki sarautar da aka basu da muhimmanci sannan su yi kokarin ganin ci gaban masarautar.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/legitnghausa

Ko a http://twitter.com/legitnghausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta LEGIT NG Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Shafin NAIJ Hausa ya koma LEGIT

Asali: Legit.ng

Online view pixel