2019: Atiku zai garzaya da kamfen dinsa zuwa Arewa ta tsakiya da kudu maso yamma

2019: Atiku zai garzaya da kamfen dinsa zuwa Arewa ta tsakiya da kudu maso yamma

Dan takarar kujeran shugaban kasa a karkashin inuwar jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP), Alhaji Atiku Abubakar, zai garzaya da kamfen dinsa zuwa yankin arewa maso tsakiya a yau Laraba, 5 ga watan Disamba.

Jaridar Punch ta ruwaito cewa za’a gudanar da gangamin arewa maso tsakiya ne a jihar Kwara.

Ku tuna cewa Atiku ya fara kamfen dinsa a yankin Arewa maso yamma wanda aka gudanar a Sokoto a ranar Litinin, 3 ga watan Disamba.

2019: Atiku zai garzaya da kamfen dinsa zuwa Arewa ta tsakiya da kudu maso yamma
2019: Atiku zai garzaya da kamfen dinsa zuwa Arewa ta tsakiya da kudu maso yamma
Asali: Facebook

An kuma tattaro cewa za’a gudanar da na kudu maso yamma a Ibadan, jihar Oyo a ranar Alhamis, 6 ga watan Disamba.

KU KARANTA KUMA: BMO ta nemi APC ta haramtawa gwamnonin jam'iyyar 2 yin takarar sanata

Daraktan labarai na kungiyar kamfen din PDP, Mista Kola Ologbondiyan; da kakakin PDP reshen jihar Kwara, Mista Tunde Ashaolu, sun tabbatar da lamarin.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=ng.legit.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng