Tambuwal, Namadi, Makarfi sun baiwa Atiku tabbacin zabubbukan jama'ar Arewa maso yamma

Tambuwal, Namadi, Makarfi sun baiwa Atiku tabbacin zabubbukan jama'ar Arewa maso yamma

Gwamnan jihar Sokoto, kuma shugaban kamfen Atiku a arewa maso yamma, Aminu Waziri Tambuwal, yace mutanen arewa za su zabi jam'iyyar PDP duk da maganganun ake radawa.

Yayinda yake gabatar da sakon maraba a taron yakin neman zaben kujeran shugaban kasan Atiku Abubakar a Sokoto ranan Litinin, Tambuwal yace yan Najeriya sun dade suna jiran kwararren mutum wanda zai shugabancesu.

Yace: "Idan aka zabi Atiku, zai kawo sauyi bangaren aikin noma, ilimi, samar da aiki yi ga matasa da tabbatar da bin doka da oda."

Tambuwal, Namadi, Makarfi sun baiwa Atiku tabbacin zabubbukan jama'ar Arewa maso yamma
Tambuwal, Namadi, Makarfi sun baiwa Atiku tabbacin zabubbukan jama'ar Arewa maso yamma
Asali: Facebook

Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Ahmed Makarfi; tsohon gwamnan jihar Jigawa, Sule Lamido; tsohon minista, Kabiru Tanimu; tsohon mataimakin shugaban kasa, Namadi Sambo; sun bukaci mutanen yankin Arewa maso yammacin Najeriya.

Tambuwal, Namadi, Makarfi sun baiwa Atiku tabbacin zabubbukan jama'ar Arewa maso yamma
Tambuwal, Namadi, Makarfi sun baiwa Atiku tabbacin zabubbukan jama'ar Arewa maso yamma
Asali: Facebook

Mun kawo muku rahoton cewa tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan da wasu manyan mambobin jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP), sun bi sahun dubban masoya a ranar Litinin, 3 ga watan Disamba, a Sokoto don kaddamar da kamfen din arewa maso yamma na dan takarar shugaban kasa, Atiku Abubakar.

Sanarwa: Shafin Naij.com Hausa shine yanzu ya koma Legit.ng Hausa, don inganta muku zafafan labarai dama kayatarwa

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/hausa.legit.ng

Twitter: https://twitter.com/hausa.legit.ng

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng