Ana kisan 'yan APC a jihohin PDP, Oshiomhole yayi zargi

Ana kisan 'yan APC a jihohin PDP, Oshiomhole yayi zargi

- Jam'iyyar APC tace jam'iyyar PDP na tsoratar da 'yayan jam'iyyar ta a jihohin da take mulka

- Wannan zargin ya biyo baya ne bayan da majalisar jihar Akwa Ibom ta kori mahukunta hudu da suka koma APC daga PDP

- Wannan shine amfani da karfin mulki gurin danne hakkin damokaradiyya

Ana kisan 'yan APC a jihohin PDP, Oshiomhole yayi zargi
Ana kisan 'yan APC a jihohin PDP, Oshiomhole yayi zargi
Asali: Depositphotos

Jam'iyyar APC tace jam'iyyar PDP tana tsoratarwa tare da tsangwamar 'yayan jam'iyyar ta a jihohin da take mulki. Shugaban jam'iyyar na kasa, Adams Oshiomhole, ya sanar da hakan ga manema labarai a ofishin jam'iyyar a daren litinin. Wannan zargin ya biyo bayan korar da majalisar jihar Akwa Ibom tayi wa mahukuntan ta hudu bayan da suka canza sheka daga PDP zuwa APC.

Mahukuntan sune NE Ntuen, Otobong Ndem, Victor Udofia da Gabriel Tobi. Shugaban jam'iyyar na kasa, ya Kwatanta hakan da amfani da karfin mulki gurin danne hakkin damokaradiyya wanda PDP keyi a jihohin da take mulki.

"Misali shine abinda ya faru a yau inda kwamishinan yan sanda suka hada baki da gwamnan jihar Akwa Ibom gurin tsige yan majalisar jiha dake jam'iyyar APC daga majalisar. Kwamishinan ya wuce makadi da rawa inda ya taimaka gurin yin abinda ba daidai ba."

Jam'iyyar All Progressive Congress (APC) tace Jam'iyyar People Democratic Party (PDP) tana tsoratar da yan kungiyar ta.Shugaban Jam'iyyar APC na kasa Adams Ishiomole ya sanar da hakan yayin da yake jawabi ga yan jaridu a sakateriar kungiyar ranar litini da dare.

Wannan zarge-zargen ya zo 'yan sa'o'i bayan majalisar dokokin jihar Akwa Ibom a ranar Litinin ta kori wasu' yan majalisa hudu da suka fice daga PDP zuwa APC. Yan Majalisan da aka koran sune Nse Ntuen, Utobong Ndem, Victor Udofia, Gabriel Toby.

Shugaban ya bayyana wannan ci gaban a matsayin takurawa. Yace "Akwai matukar damuwa da takurawa a wasu jihohin da PDP take shugabanta domin tana yin amfani da kayan aiki na jihar - tana amfani da 'yan sanda don raunana' yanci na dimokiradiyya na 'yan APC. Misalin abin da ya faru a yau a Jihar Akwa Ibom inda kwamishinan 'yan sanda na Jihar ya hada kai tare da gwamnan suka cire yan kungiyar APC daga majalisa na jihar".

Ya kara da cewa "Kwamishinan ya wuce layinsa don taimakawa ga abinda kowa ya san ba dai dai bane. Ba aikin 'yan sanda ba ne taimakawa hukumomin siyasa don cikar burinsu". Yace "Ina tsammanin muna da shari'a, muna da doka da umurni, alhakin 'yan sanda shine su bi umarnin kotu, kada su wuce shi. Idan gwamnan ya bukaci karin taimakon shari'a daga 'yan sanda, be kamata Kwamishinan ya yarda ba, amma hakan ya faru a Jihar Akwa Ibom."

Shugaban Jihar APC a Jihar Enugu ya tsere da kyar daga kisa. A Jihar Rivers, an kama wasu yan Jam'iyyar biyu kuma daya daga cikin shugabannin APC da aka sace an gano jikinsa."munyi imani waɗannan laifukan ba tsautsayi bane ko da yake ba laifin da yake tsautsayi. Mun yi mamakin jagorancin shugabanninmu, musamman a jihohi inda ba mu da gwamnoni, yadda suka ci gaba da kai hari, tashin hankali, zalunci da kisan kai, a gareni , wadannan alamun haɗari ne."

DUBA WANNAN: Sabuwar kungiyar Ta'adda ta bullo

"Na yi imanin cewa, APC za ta lashe zaben kuma duk 'yan Jam'iyyar da suka yi watsi da Jam'iyyar saboda suna so su zama shugaban kasa, za su gano cewa yayin da suke harbe-harbe zuwa kashe giwa, mutanen su ba su tunanin cewa sun cancanci karkanda kuma za su azabtar da su da katin zaben su." yace.

Sai dai jam'iyyar ta ce ta bukaci gwamnati ta binciko rikicin yan Majalisa na Akwa Ibom kuma za a gabatar da kwamishinan 'yan sandan gaban sharia. Shugaban jam'iyyar ya yarda cewa yan sanda basu da muhalli a wannan aikin saboda masu shari'a na nan.

"A tunani na ai muna da masu shari'a, muna da doka da oda kuma aikin yan sanda shine bin umarnin kotu, ba wai zaqewa ba. Idan gwamna na bukatar taimakon shari'a, amma sai yaje gurin kwamishinan yan sanda, kamata yayi kada yayi biyayya. Amma wannan shine abinda ya faru a jihar Akwa Ibom."

Wani abu da shugaban jam'iyyar yace ana wa yayan jam'iyyar shine kai musu hari, kisa da kuma tsangwama, wanda hakan bai dace ba.

"Shugaban jam'iyyar APC na jihar Enugu ya tsallake yunkurin kashe shi da akayi. A jihar Rivers ma an sace yan majalisar jihar guda biyu kuma sai aka tsinci gawar daya daga cikin su. Bazamu amince da wannan ta'addancin ba. Abin na bamu mamaki, ballantana kuma a jihohin da ba jam'iyyar mu ke mulki ba."

Shugaban jam'iyyar yace sun yanke hukuncin karar duk mai hannu a cikin wannan ta'addancin, dole ne a mutunta hakkin duk wani Dan Najeriya kuma a duk jam'iyyar da yake.

Sanarwa: Shafin Naij.com Hausa shine yanzu ya koma Legit.ng Hausa, don inganta muku zafafan labarai dama kayatarwa

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/hausa.legit.ng

Twitter: https://twitter.com/hausa.legit.ng

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com

Asali: Legit.ng

Online view pixel